Labarai

CP Bakori ya yaba wa wata mace kan gyara ofishin shiyya na rundunar a Kano

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kwamishinan 'Yan sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori ya gabatar da wasiƙar godiya ga Hajiya Hajara Abdullahi ta Diso Quarters da ke Ƙaramar Hukumar Gwale a jihar, yayin yaba wa ƙoƙarinta na taimaka wa al'umma musamman kan gyara ofishin 'yan sanda na Shiyyar Gwale da ta gudanar. Ya ce, wannan hoɓɓasa da Hajiya Hajara ta yi na wakiltar gagarumar gudumawa ga harkar tsaro a yankin. A cewarsa, tana bayar da tallafi ga ayyukan shiyyoyin 'yan sanda a sassan jihar da nufin inganta wuraren ayyukan jami'ai da bunƙasa lamuran hidimta wa al'umma. Da yake damƙa…
Read More

Shugaban sojoji ya je ta’aziyya bayan harin ‘yan bindiga ya yi ajalin babban limami da wasu 27 a Sakkwato

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kimanin mutane 28 ciki har da limamin Masallacin Izala na Ungushi, Imam Aliyu ne aka halaka a lokacin da wasu 'yan bindiga suka farmaki jama'a a ƙauyen Ungushi da ke Ƙaramar Hukumar Kebbe ta Jihar Sakkwato a daren Litinin. Da yake tabbatar da labarin, Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Sakkwato, DSP Ahmed Rufa'i, ya ce yana da wuya a iya gano ainihin adadin waɗanda iftila'in ya shafa. Saidai, ya ce an gano gawarwaki guda 28 bayan aukuwar lamarin. Mazauna sun ce maharan sun afka wa ƙauyen ne da dare, inda suka buɗe wa jama'a…
Read More

WAEC na fuskantar sabon ƙalubale kan sakamakon jarrabawar 2026 yayin zargin saɓa wa dokoki

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Shirya Jarrabawar Yammacin Afirka (WAEC), ta fara fuskantar bincike kan sakamakon da ta fitar a kwanan nan na jarrabawar kammala sakandare ta WASSCE ta 2026 yayin da jagororin makarantu da masu kira ga neman ilimi suka yi zargin saɓa wa ƙa'idoji da matsalolin sadarwa sanadiyyar amfani da cibiyoyin kwamfuta (CBT). Hakan na zuwa ne bayan da jagororin makarantu da dama suka yi ƙorafi da iƙirarin da masu kira ga neman ilimi suka gabatar cewa wasu zaƙaƙuran ɗalibai sun samu maki ƙasa da yadda ake tsammani, bisa la'akari da ƙoƙari da kuma abin da…
Read More
Zuwa ga masu shirin aure (II)

Zuwa ga masu shirin aure (II)

Assalamu alaikum, kamar yadda muka faɗa a makon da ya gabata cewa, za mu ci gaba daga inda muka tsaya. Abu na biyu da zan gaya muku shi ne yana da kyau ku fahimci cewa waɗannan abubuwa ba a samunsu haka kawai, wato ba sa samun mutum haka kawai, dole ne ku yi ƙoƙari wajen samar da su. Hanyar samar da su kuwa ita ce dukkan ma'auratan su so junansu. Wataƙila ku tambaya ta ya ya? Kamar yadda ake cewa ne, "ba a iya tabbatar da so da ƙauna ta hanyar ƙarfi da tursasawa", lalle haka ne don kuwa so…
Read More
Yunƙurin Tinubu na farfaɗo da tsaron Nijeriya 

Yunƙurin Tinubu na farfaɗo da tsaron Nijeriya 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A yayin da nake wannan rubutun iyalai da ’yan uwan jami’an ’yan sandan nan su 10 da ’yan ta'adda suka hallaka a yayin artabun da suka yi a yankin Makuku na ƙaramar Hukumar Sakaba a Jihar Kebbi, suna nan cikin alhini da jimami, sakamakon kisan gillar da aka yi musu. Wannan babban koma baya ne ga harkar tsaro, da kuma yaƙin da ake yi da ’yan ta'adda da masu ɗauke da makamai suna cutar da al'umma. A yayin da ake kukan jami’an tsaro sun yi ƙaranci, ’yan ta'adda na samun goyon bayan matasa zauna-gari-banza don cimma…
Read More
Ana zargin rufe otel ɗin Sandaji a Lafia na da alaƙa da siyasa

Ana zargin rufe otel ɗin Sandaji a Lafia na da alaƙa da siyasa

Daga JOHN D. WADA a Lafia Rufin wucin gadi na otel ɗin Sandanji da ke Lafia wanda Alhaji Abubakar Shehu Usman na rukunin kamfanonin Sandanji Group of Companies ke mallaka ya haifar da ayar tambayoyi kan ko wannan matakin gwamnatin jihar lamari ne na tsaftar muhalli kawai ko kuma yana da alaƙa da siyasa. A kwanan nan ne dai gwamnatin jihar ta Nasarawa ta ma'aikatar muhalli da albarkatun ƙasa ta rufe otel ɗin bayan wani ambaliyar ruwa da ya auku a kewayen wurin da otel ɗin ya biyo bayan wani ziyarar duba da ido da kwamishiniyar ma’aikatar muhallin ta jihar…
Read More
Ba a ƙetare Kudancin Nasarawa ba a kasafin 2026, inji Akolo Peters

Ba a ƙetare Kudancin Nasarawa ba a kasafin 2026, inji Akolo Peters

Daga JOHN D. WADA a Lafia Daraktan kasafi a ma’aikatar kuɗi da kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki ta jihar Nasarawa Akolo Peters Ataka ya musanta zargin cewa gwamnatin jihar ta yi watsi da mazaɓar Sanatan Kudancin jihar musamman ƙananan hukumomin Obi da Doma da Awe da kuma Keana a cikin kasafin kuɗin shekarar 2026. Peters Ataka wanda ya bayyana kasafin a matsayin “kasafin haɗin kai na dabaru”, yana mai cewa an tsara shi ne domin ya shafi kowane fanni a jihar kuma ya tabbatar da cewa mazaɓu uku na sanata da ake dasu a jihar duk sun amfana da shirye-shirye…
Read More
Dakta Steven ya gargaɗi matasa kan tayar da zaune tsaye

Dakta Steven ya gargaɗi matasa kan tayar da zaune tsaye

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Babban sakatare a ma’aikatar matasa da raya wasanni ta jihar Nasarawa Dakta Stephen Iliya Sasetu ya yi kira na musamman da a riƙa shigar da matasa cikin ayyuka masu amfani domin daƙile zaman banza da kuma inganta zaman lafiya a jihar. Sasetu ya bayyana haka ne ranar Talata na mako da ake ciki yayin da yake jawabi ga manema labarai a ofishinsa dake ma'aikatar a Lafia gabanin gudanar da ayyukan bikin ranar matasa ta duniya na bana. Yace akwai buƙatar a haɗa kan matasa tare waje guda a kuma yi musu jawabi don a…
Read More

Mu na nazarin sakamakon zaɓen Osun – APC

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Jam’iyyar APC a Jihar Osun, ta ce tana nazari kan sakamakon zaɓen gwamnan jihar na 2026 da aka kammala a kwanan nan, domin tantance matakin da za ta ɗauka na gaba. Daraktan yaɗa labaranta, Kola Olabisi ne ya bayyana haka a wata takarda da ya fitar a ranar Lahadi a Osogbo. A cewarta: "Babu yadda za a yi a ce an kammala zaɓe ba tare da aiwatar da dukkan damar da doka ta bayar ba na gyara ababen da suka saɓa wa tsari da aka gano yayin haka, kamar yadda Dokar Zaɓe ta 2026…
Read More

NFF ta sallami tawagar jagorancin Super Falcons ta Koci Madugu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kwamitin Zartarwa na Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Ƙasa (NFF), ya tsige tawagar gudanar da harkokin 'yan wasan Super Falcons ƙarƙashin jagorancin Justine Madugu, hukuncin da ya fara aiki a nan take. NFF ta sanar da haka ne a wata sanarwa da ta wallafa a sahihin shafinta na X a ranar Litinin. Super Falcons ta shiga mawuyacin hali yayin buga wasannin gasar Kofin Ƙasashen Afirka na Mata WAFCON, wanda aka gudanar a ƙasar Moroko. Nijeriya ta shiga gasar ne a matsayin wadda take riƙe da kofin kuma ta lashe har sau goma a tarihinta. Saidai…
Read More