Labarai

Sama da farfesoshi da lakcarori 200 na Jami’ar Kaduna sun yi murabus yayin da ASUU ta yi barazanar shiga yajin aiki

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Malaman jami'a da suka haɗa da masu muƙamin farfesa da wasu sama da guda 200 ne suka bar Jami'ar Kaduna KASU, bisa rashin ingancin lamuran gudanarwa da rashin aiwatar da yarjejeniyar Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Ƙasa (ASUU) ta 2025, inji reshen ƙungiyar na KASU. Rahotanni sun bayyana cewa ASUU reshen KASU ta bayar da wa'adin sati biyu ga hukumomin jami’o’i da sauran masu ruwa da tsaki da su fara aiwatar da yarjejeniyar yadda aka tsara ta, tana mai gargaɗin cewa rashin yin hakan ka iya haifar da yajiin aikin sai baba-ta-gani…
Read More

Dakarun tsaro sun ceto mutum tara bayan daƙile harin ‘yan bindiga a hanyar Zamfara

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun Sashe ne 2 na Atisayen FANSAR YAMMA, sun yi nasarar daƙile wani harin 'yan ta'adda na garkuwa da mutane da dama a Unguwar Rogo da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda ta Jihar Zamfara, inda suka yi nasarar ceto wasu mutane guda tara, saidai maharan sun tsere da uku a yayin haka. Rahotanni sun bayyana cewa, ana zargin maharan yaran jagoran 'yan ta'adda mai suna Malam Shu'aibu ne, waɗanda suka ƙaddamar da harin da nufin ramuwa akan atisayen sojoji na kwanan nan kan dabar da masu taimaka mata ciki har da kama masu tsegumi…
Read More

‘Yan sanda sun tabbatar da harin ‘yan ta’adda a Sakkwato

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Sakkwato ta tabbatar da cewa wasu da ake zargin 'yan ta'addan Lakurawa ne sun kai wani hari a garin Kebbe a ranar Juma'a, inda ta ce jami'an tsaro sun mayar da martani kuma an tura ƙarin wasu a yankin. Haka kuma, rundunar ta ce babu wani farar hula da aka halaka ko jikkata harin saɓanin wasu rahotanni da ke nuna 'yan ta'addar sun halaka mutane da dama. Wasu rahotanni da aka wallafa bayan aukuwar lamarin sun bayyana cewa an halaka soja guda huɗu a yayin arangamar, amma Rundunar Soji…
Read More
Kwamred Maiwada ya zama shugaban NLC na riƙo a Katsina

Kwamred Maiwada ya zama shugaban NLC na riƙo a Katsina

ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa reshen jihar Katsina, ta naɗa Kwamared Nasiru Wada Mai'adua a matsayin zhugaban ƙungiyar na riƙon ƙwarya. Naɗa shi shugaban ƙungiyar na riƙon ƙwarya ya biyo bayan, aje muƙamin da shugaban ƙungiyar na Jiha Comrade Hussaini Hamisu Yanduna ya yi bayan zama babban Sakatare a Gwamnatin Jihar Katsina. Kwamred Nasiru Wada Mai'adua kafin naɗa shi muƙamin shugaban ƙungiyar ƙwadagon na riƙon ƙwarya, shine shugaban ƙungiyar ma'aikatan ƙananan hukumomi ( NULGE )ta Jihar Katsina.
Read More
Mutane biyar sun mutu sakamakon rushewar gine-gine a Kano

Mutane biyar sun mutu sakamakon rushewar gine-gine a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Mutane biyar ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu 10 suka tsira bayan rushewar wasu gine-gine guda biyu da suka faru a ƙananan hukumomin Kumbotso da Fagge na Jihar Kano. Lamarin ya faru ne a ranar Asabar a unguwar Gaida da ke Kumbotso, da kuma Kurna da ke Fagge. Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano ta ce ta samu kiran neman agaji da misalin ƙarfe 2:34 na rana da kuma 2:40 na rana, bi da bi. A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Abdullahi, ya…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe mutum bakwai a Katsina

‘Yan bindiga sun kashe mutum bakwai a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Ƙasurgumin ɗan bindiga Kachalla Maha da mutanen sa sun kashe mutum bakwai a ƙauyen Guru garin Sukuntuni na ƙaramar hukumar Kankia. A hira da yayi a wata kafar sadarwa ta JBC Malam Abubakar Tijjani daga garin Sukuntuni ya bayyana cewa Kachalla da mutanen sa sun shiga gida gida su kai ta harbin mutanen ƙauyen tare da Kona Gidaje. Yace wannan hari da Kachalla ya kai a ƙauyen ramakon gayyace domin a kwanakin baya sun shiga ƙauyen da niyar satar dabbobi amma mutanen ƙauyen su kai fito na fito da 'yan bindigan har ta kai ma…
Read More

An kama budurwa a Kebbi kan zargin satar jariri da juna biyun bogi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan Sanda a Jihar Kebbi, ta ce ta kama wata mata mai shekaru 19 a Ƙaramar Hukumar Zuru da ke jihar bisa zargin ta da sace wani sabon jariri da gabatar da shi ga mijinta a matsayin nata. Al'amarin ya auku ne a ranar 23 ga Yuli, 2025, a lokacin da wadda ake zargin ta ziyarci wata mai suna Fatima Muhammad jim-kaɗan bayan ta haihu, inda ta taimaka mata da wasu ayyuka ciki har da ɗebo ruwa. A cewar 'yan sanda, wadda ake zargin ta yi amfani da damar hakan ne wajen tserewa…
Read More

Kakakin majalisar dokokin Edo, Blessing Agbebaku ya yi murabus yayin yunƙurin tsige shi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kakakin Majalisar Dokoki na Jihar Edo, Blessing Agbebaku ya sauka daga muƙaminsa yayin da ake tsaka da zargin wasu mambobin majalisar na shirin tsige shi. Rahotanni sun bayyana cewa, ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Akoko Edo ta II, Yekini Idaiyi ne aka rantsar a matsayin sabon kakakin bayan matakin na Agebakun. Mai taimaka wa Agbebaku kan harkokin yaɗa labarai, Ivy Ebojele ne ya tabbatar da murabus ɗin mai gidan nasa a wani rubutu da ya ɗora a kafar Facebook a ranar Litinin, inda ya ce za a fitar da ƙarin bayani kan al'amarin a…
Read More
‘Yan sanda sun kama wani mutum bisa laifin cin mutuncin Alqur’ani a Kebbi

‘Yan sanda sun kama wani mutum bisa laifin cin mutuncin Alqur’ani a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Rundunar 'yan sandan jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Abubakar Musa ɗan asalin ƙauyen Rafin Mose da ke ƙaramar hukumar Zuru bisa ga laifin cin mutuncin Alqur'ani mai tsarki. Da ya ke zantawa da wakilin Jaridar Blueprint Manhaja, Kakakin rundunar 'yan sanda Sufurtanda Bashir Usman ya bayyana cewa an kama wannan mutum ne bisa zargin haɗa baki da Rabi'u Tela da matar sa Zara'u Hassan da kuma Hamza Zango bisa ga laifin surkulle da keta haddin al'umma da kuma cin mutuncin Alqur'ani mai tsarki. Ya ƙara da cewa bincike ya nuna sauran abokan…
Read More

Cardoso, Ojulari da Tantita za su halarci taron Karramawa na Blueprint gobe

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Mista Olayemi Cardoso; Shugaban Babban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), Injiniya Bashir Bayo Ojulari da Kamfanin Tantita Security Services suna daga cikin sanannun mutane da ƙungiyoyin da za a karrama a babban taron shekara-shekara na bayar da lambobin yabo da Kamfanin Jaridun Blueprint Newspapers Limited zai jagoranta a gobe Talata, 18 ga Agusta, 2026. Taron, wanda za a gudanar a ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre, Abuja, zai haɗa manyan jami’an gwamnati, jagororin siyasa, jagororin kamfanoni, masana harkar tsaro, 'yan difulomasiyya, malamai, wakilan ƙungiyoyin al'umma,…
Read More