Labarai

‘Yan sanda sun daƙile yunƙurin kai harin ‘yan bindaga a Katsina

‘Yan sanda sun daƙile yunƙurin kai harin ‘yan bindaga a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina 'Yan sanda sun daƙile yunƙurin hare haren 'yan bindiga da satar mutane a ƙauyen Fulalawa da ke ƙaramar hukumar Musawa a Jihar Katsina. A wata sanarwa jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yan sanda a Katsina DSP Abubakar Sadiq Aliyu,ya ce bayan samun bayanan sirri cewar 'yan bindiga ɗauke da manyan makamai sun Kai hari har da satar mutane a ƙauyen Fulalawa,nan take 'yan sanda da taimakon jami'an tsaro na CWC suka fara ɓarin wuta da ya tilastawa 'yan bindigan ja da baya,wasu a cikin su ana zargi sun gudu suna ɗauke da manyan raunuka.…
Read More
Masana’antar sufurin jiragen saman Nijeriya na iya durƙushewa cikin kwanaki 30 – Shugaban Air Peace

Masana’antar sufurin jiragen saman Nijeriya na iya durƙushewa cikin kwanaki 30 – Shugaban Air Peace

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban Kamfanin Jirgin Sama na Air Peace, Allen Onyema, ya yi gargaɗin cewa, masana’antar sufurin jiragen sama ta Nijeriya na fuskantar yanayi na barazana, yana mai cewa wasu kamfanonin jiragen saman cikin gida na iya durƙushewa cikin kwanaki 30 masu zuwa matuƙar ba a ɗauki matakan gaggawa wajen magance matsalolin da ke addabar masu gudanar da harkar ba. Onyema ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai a wajen ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar Shugaban Kamfanin Jiragen Sama na Med-View, Muneer Bankole, mai suna Pathways, Pilgrimage and Destiny. Shugaban Air Peace ya ce…
Read More
EFCC ta gurfanar da ’yan canji ba bisa ƙa’ida ba

EFCC ta gurfanar da ’yan canji ba bisa ƙa’ida ba

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Masu Yi wa Tattalin Arzikin ƙasa Ta’annati (EFCC) ta gurfanar da wasu mutane huɗu a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke zama a Ikoyi, Jihar Legas, inda aka yanke musu hukuncin ɗaurin watanni biyu zuwa shida bisa laifin gudanar da harkokin musayar kuɗin waje ba ta hanyar da doka ta tanada ba, da kuma safarar takardun kuɗin naira ba bisa ƙa’ida ba. Waɗanda kotun ta samu da laifi su ne Ahmad Umar Baros, Aminu Umar Injay, Yusuf Suleimon da Olasunbo Sholanke. Hukuncin ya fito ne daga Mai Shari’a F.N. Ogazi, bayan Daraktar Yankin…
Read More
Hukumar NERC ta tsige daraktocin Kamfanin Rarraba Wutar Lantaki na Kaduna kan bashin Naira biliyan 456.5

Hukumar NERC ta tsige daraktocin Kamfanin Rarraba Wutar Lantaki na Kaduna kan bashin Naira biliyan 456.5

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar Kula da Harkokin Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta rushe kwamitin gudanarwar Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna (KAEDC), sakamakon tarin bashin da kamfanin ya kasa biyan kasuwar wutar lantarki wanda ya kai kusan Naira biliyan 456.5. Hukumar ta kuma naɗa wani kwamitin riƙon ƙwarya na musamman, tare da umartar a fara wani tsari na gaskiya da gasa domin nemo sabon babban mai zuba jari da zai karɓi ragamar kamfanin. Matakin na NERC yana ƙunshe ne cikin Umarni mai lamba NERC/2026/086, mai taken “Umarni kan shiga tsakani a harkokin Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna…
Read More
Gwamnatin Enugu ta fara aikin samar da lantarki na sama da awanni 20 kullum

Gwamnatin Enugu ta fara aikin samar da lantarki na sama da awanni 20 kullum

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Enugu ta fara wani garaumin aikin gina sabbin layukan rarraba wutar lantarki guda uku masu ƙarfin 33KV, da nufin inganta samar da hasken wutar lantarki mai ɗorewa, sauƙin samu da kuma inganci a wasu yankuna na jihar. Aikin, wanda zai samo wuta daga Tashar Wutar Lantarki ta Ugwuaji, zai amfani al’ummomin ƙananan hukumomin Nkanu East, Nkanu ta Yamma, Aninri da Awgu. Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa, kafin ƙaddamar da aikin, an gudanar da taron masu ruwa da tsaki kan harkar wutar lantarki a Cibiyar Taro ta ƙasa da ƙasa da ke…
Read More
Ya kamata a nesanta addini da ƙazantar siyasar jam’iyya – Gumi ga Jingir

Ya kamata a nesanta addini da ƙazantar siyasar jam’iyya – Gumi ga Jingir

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Malamin addinin Musulunci da ke zaune a Kaduna, Sheikh Dr Ahmad Gumi, ya yi kira da a nesantar da addini daga siyasar jam’iyyu, yana mai cewa bai kamata a jawo batun addini cikin fafatawar siyasa a Nijeriya ba. Gumi ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook da aka tabbatar a ranar Litinin, yayin da yake mayar da martani kan kalaman da ake dangantawa da Sheikh Sani Yahaya Jingir, Shugaban ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS). Jingir ya yi waɗannan kalamai ne a wani taron bikin auren gata da…
Read More
Kuri’a ɗaya ta isa ka kwashe komai – Obasanjo ya caccaki tsarin dimukraɗiyyar Nijeriya

Kuri’a ɗaya ta isa ka kwashe komai – Obasanjo ya caccaki tsarin dimukraɗiyyar Nijeriya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Tsohon Shugaban ƙasar Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya soki tsarin dimukraɗiyyar da ake amfani da shi a yawancin ƙasashen Afirka, yana mai cewa tsarin dimukraɗiyyar sassaucin ra’ayi da aka gada daga ƙasashen Yamma bai dace da yanayin Afirka ba, kuma ya haifar da siyasar ‘mai nasara ya kwashe komai’. Obasanjo ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin taron tattaunawar dimukraɗiyya na gidauniyar tsohon Shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na shekarar 2026, wanda aka gudanar a Bauchi, babban birnin Jihar Bauchi. Tsohon shugaban ya ce tsarin dimukraɗiyyar Yamma da ƙasashen Afirka suka gada bai ginu kan tarihi, al’adu…
Read More
Ban taɓa cin amanar matata ba tun bayan aurenmu – Rauf Aregbesola

Ban taɓa cin amanar matata ba tun bayan aurenmu – Rauf Aregbesola

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Sakataren Jam’iyyar ADC na ƙasa, kuma tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, ya bayyana cewa tun bayan da ya auri matarsa, Sherifat, bai taɓa yin wata alaƙar soyayya ko ta kusanci da wata mace ba. Aregbesola ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar ADC a wani gangamin yaƙin neman zaɓe da aka gudanar a ƙaramar Hukumar Ejigbo ta Jihar Osun, gabanin zaɓen gwamnan jihar da aka shirya gudanarwa a ranar 15 ga Agusta, 2026. Tsohon gwamnan, wanda ya yi jawabin ne da harshen Yarbanci, ya ce tsoron Allah da kuma alƙawarin…
Read More
Tinubu ya yi kira ga malaman addini da su yi amfani da muryarsu wajen yaƙi da ta’addanci

Tinubu ya yi kira ga malaman addini da su yi amfani da muryarsu wajen yaƙi da ta’addanci

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga malaman addini a Nijeriya, Afirka da sauran sassan duniya da su ci gaba da anfani da muryoyinsu kan yaki da ta’addanci, garkuwa da mutane, da kuma amfani da addini wajen kashe-kashe da tashin hankali. Tinubu ya ce babu wata ibada ta gaskiya da za ta samu ci gaba ta hanyar zubar da jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba. Shugaban ƙasar ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Kano, a cikin saƙon fatan alheri da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata…
Read More
A Ringim shekaru 50 al’umma na fama da matsalolin lafiya — Garba Dabi

A Ringim shekaru 50 al’umma na fama da matsalolin lafiya — Garba Dabi

Daga ABDULLAHI SANI DOGUWA a Kano Shugaban ƙaramar Hukumar Ringim ta Jihar Jigawa, Hon. Badamasi Garba Dabi, ya bayyana cewa al’ummar yankin sun shafe kusan shekaru 50 suna fama da matsaloli a fannin kiwon lafiya, kafin zuwansa shugabancin ƙaramar hukumar. Da yake jawabi ga manema labarai a ofishinsa da ke Sakatariyar ƙaramar Hukumar Ringim, Hon. Badamasi Garba Dabi ya ce tun bayan da Allah (A.W.T) Ya ɗora masa nauyin jagorantar al’ummar yankin, ya mayar da hankali wajen sauraron koke-kokensu da kuma nemo hanyoyin magance matsalolin da suka daɗe suna addabar su. Ya ce daga cikin muhimman fannoni da ya ba…
Read More