Babban Labari

Yadda rikita-rikitar digiri ɗan jabu ta ruɗa Nijeriya

Yadda rikita-rikitar digiri ɗan jabu ta ruɗa Nijeriya

*Badaqalar ta shafi jami’o’i 78 *An cafke jami’ai bisa zargin hannunsu *Hukumar NYSC ta farga Daga MAHDI M. MUHAMMAD A farkon makon nan ne Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta dakatar da amincewa da takardar shaidar digiri daga wasu jami’o’in kasashen waje da ma masu cibiya a cikin gida. Umarnin na qunshe ne a cikin wata sanarwa ne da aka fitar a ranar Talata, 2 ga Janairu, 2023, mai dauke da sa hannun Augustina Obilor-Duru a madadin Daraktan Yada Labarai Da Hulda Da Jama’a Na Ma’aikatar Ilimi Ta Tarayya. Gwamnati ta koka da cewa "wasu 'yan Nijeriya suna amfani da hanyoyin da…
Read More
Almundahana: Yadda EFCC ke ƙoƙarin titsiye tsofaffin jami’an Buhari mata

Almundahana: Yadda EFCC ke ƙoƙarin titsiye tsofaffin jami’an Buhari mata

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A cikin makon nan ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Shugabar Hukumar Shirin Bada Tallafi da Dogaro da Kai, wato ‘National Social Investment Programme Agency’ (NSIPA), inda a gefe guda kuma tun a makon jiya Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati ta mika goron gayyatarta ga tsohuwar Ministar Jinkai da Agaji a lokacin tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, wato Sadiya Farouq kan zargin ta da hannu a badakalar Naira biliyan 37.1. A bangaren Halima Shehu ta hukuma NSIPA, wacce ke karkashin Ma’aikatar Jinkan, bayanai sun ce hukumar…
Read More
Fassarar jawabin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a sabuwar shekarar 2024

Fassarar jawabin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a sabuwar shekarar 2024

Ya ku `yan uwana 'yan Nijeriya, ina cike da farin ciki a yayin da nake wa Ilahirinmu, matasa da tsofaffi maraba da shigowa sabuwar shekara ta dubu biyu da ashirin da hudu. Dole ne mu daga hannuwanmu sama mu gode wa Allah Madaukakin Sarki saboda albarkar da Ya yi wa kasarmu da kuma rayukan mu a cikin shekarar da ta gabata wato shekara ta dubu biyu da ashirin da uku. Kodayake shekarar da ta gabata na kunshe da kalubale da dama, amma duk da haka an yi abubuwan alheri masu yawa, ciki har da mika mulki daga tsohuwa zuwa sabuwar…
Read More
Tinubu ya rattaɓa hannu kan kasafin 2024

Tinubu ya rattaɓa hannu kan kasafin 2024

Daga BASHIR ISAH    Shugaban Kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin 2024 na Naira tirilyan 28.7 wanda hakan ya sanya  kasafin zama doka. A ranar Litinin da ta gabata Tinubu ya sanya wa kasafin hannu da misalin karfe 2:00 na rana a ofishinsa, inda aka shirya kwarya-kwaryar biki wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnatinsa. Mahalarta bikin sun hada da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio; Shugaban Majalisar Wakilai, Hon Tajudeen Abbas; Ministan Kudi, Mr Wale Edun. Sauran sun hada da Ministan Kasafi da tsare-tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Atiku Bagudu; Mai bai wa Shugaban Shawara Kan Sha’anin Tsaro (NSA),…
Read More
Don amfanin ƙasa na ɗauki tsauraran matakai – Tinubu

Don amfanin ƙasa na ɗauki tsauraran matakai – Tinubu

Daga BASHIR ISAH Shuagaban Kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa, tsauraran matakan da ya dauka tun bayan da ya karbi ragamar mulkin kasa, ya yi hakan ne domin ceto Nijeriya daga fadawa halin ha’ula’i. Tinubu ya bayyana haka ne a jawabin sabuwar shekarar da ya yi wa ‘yan kasa da safiyar ranar Litinin, wanda aka yada kai tsaye a kafafen yada labarai. A cewarsa, “Dukkan abin da na yi a ofis, duk wani mataki da na dauka, duk wata tafiya da na yi zuwa wajen kasa tun bayan da na shiga ofis ran 29 ga Mayun 2023, na yi hakan…
Read More
Gobe Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabin sabuwar shekara

Gobe Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabin sabuwar shekara

Daga BASHIR ISAH Gobe Litinin, 1 ga Janairu, ake sa ran Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai yi wa 'yan kasa jabi albarkacin shiga sabuwar shekarar 2024. Kakakin Shugaba Kasa, Ajuri Ngelale, ya bayyana a sanarwar da ya fitar yau Lahadi cewa, da karfe 7:00 na safe ne ake sa ran Shugaban ya gabatar da jawabin nasa. "Don haka ake kira ga tashoshin talabijin da na rediyo da sauran kafafen yada labarai da su jona da tashoshin talabijin da rediyo na gwamnati don yada jawabin," in ji shi. Wannan shi ne karon farko da Tinubun zai yi wa 'yan kasa…
Read More
Waiwayen muhimman abubuwan da suka faru a 2023

Waiwayen muhimman abubuwan da suka faru a 2023

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shekara ta 2023 ta zo qarshe, kuma daya daga cikin abubuwan da za a iya cewa a kanta shi ne, shekarar cike ta ke da al’amura masu kyau da munana da suka afku. Batutuwa kamar tsadar rayuwa, rikice-rikicen ’yan Boko Haram da ISWAP, ’yan bindiga masu satar mutane da kuma rikata-rikitar siyasa sun mamaye yawancin kwanakin shekarar. Bisa ga dukkan alamu, shekarar 2023 ta zama abar ban tsoro. Za a tuna ta a matsayin shekarar kunci. Hatta Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi ishara da hakan a sakonsa na Kirsimeti, inda ya ce, shekara ce ta…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ondo, Oluwarotimi Akeredolu ya rasu

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ondo, Oluwarotimi Akeredolu ya rasu

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Ondo, Oluwarotimi Akeredolu, ya rasu a safiyar Laraba bayan fama da rashin lafiya. Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) ya rawaito cewa, Gwamnan ya rasu ne a ƙasar Jamus. Marigayin ya bar duniya yana da shekara 67, bayan shafe lokaci yana fama da cutar kansar jini da kansar mafitsara. Rasuwar tasa na zuwa ne kimanin mako biyu, bayan Gwamna Akeredolu ya rubuta wasikar tafiya neman lafiya, inda ya mika ragamar mulkin jihar ga mataimakinsa, Lucky Aiyedatiwa. Marigayin ya shafe kusan wata uku a kasar Jamus yana jinya, daga bisani ya koma Nijeriya a watan Satumban…
Read More
Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Na’Abba ya kwanta dama

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Na’Abba ya kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa tsohon Shugaban Majalisar Wakilai ta Kasa, Alhaji Ghalli Na’abba rasuwa. Duk da dai babu cikakken bayani game da rasuwar tasa, amma majiya mai tushe ta ce marigayin ya rasu ne da misalin karfe 3:00 na daren da ya gabata. A shekarar 1999 ya zama dan majalisa mai wakiltar Kano Municipal a Majalisar Wakilai, inda daga bisani ya samu nasarar zama Kakakin Majalisar. An haifi marigayin ne a 1958 a zuri'ar Alhaji Umar Na’Abba, a yankin Tudun Wada, Kano.
Read More
Kisan bom: Al’ummar Tudun Biri sun yi tutsun zuwa kotu

Kisan bom: Al’ummar Tudun Biri sun yi tutsun zuwa kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Al’ummar ƙauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna sun yi tutsu bisa ƙarar da aka shigar da sunansu a Babbar Kotun Tarayya Kaduna ta neman Gwamnatin Tarayya ta biya su diyyar Naira biliyan 33 kan kuskuren harin boma-bomai da aka kai, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100 tare da jikkata wasu da dama. Dagacin ƙauyen Tudun Biri, Malam Balarabe Garba, ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar godiya ga Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, inda ya ce, sun samu labarin cewa, wasu sun garzaya kotu a madadinsu.…
Read More