Babban Labari

EFCC ta yi sabon shugaba

EFCC ta yi sabon shugaba

Daga AISHA ASAS Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin sabon Shugaban Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC). Sanatocin sun shafe sa'o'i biyu suna tantance Bawa kafin daga bisani suka tabbatar da shi a sabon matsayin nasa. Yayin da ake tantance shi, Bawa ya bai wa majalisar tabbacin cewa zai yi aiki tukuru don gyara wa hukumar zama ta hanyar inganta harkokinta kafin ƙarewar wa'adin jagorancinsa. Bawa ya ce zai yi aiki tare da waɗanda suka dace a sassan duniya domin tabbatar da Nijeriya ta amfana da dukiyoyinta da aka…
Read More
Ortom ya nemi Bala ya bai wa ‘yan ƙasa haƙuri kan furucinsa

Ortom ya nemi Bala ya bai wa ‘yan ƙasa haƙuri kan furucinsa

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom, ya buƙaci takwararnsa na jihar Bauchi, Bala Mohammed, da ya fito ya bai wa 'yan Nijeriya haƙuri game da furucin da ya yi na goyon bayan Fulani makiyaya su riƙa amfani da bindiga wajen kare kansu. Ortom ya buƙaci haka ne yayin taron manema labarai da ya gudana a Makurdi a Litinin da ta gabata inda ya ce akwai buƙatar Gwamna Bala ya bada haƙuri domin sanyaya zukatan waɗanda suka rasa 'yan'uwa sakamakon ayyukan ɓatagarin Fulani makiyaya. Kazalika, Ortom ya buƙaci Gwamna Bala da ya yi koyi da takwarorinsa na Kano da…
Read More
Buhari da Lawan sun nuna alhininsu kan haɗarin jirgi a Abuja

Buhari da Lawan sun nuna alhininsu kan haɗarin jirgi a Abuja

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa kan haɗarin jirgin saman sojoji da ya auku Lahadin da ta gabata a Abuja. Sanarwar da hadimin Buhari kan sha'anin yaɗa labarai, Femi Adesina ya fitar, ta nuna yadda Shugaba Buhari ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalai, 'yan'uwa da abokan aikin sojojin da suka rasu a haɗarin. Sanarwar ta ce Buhari ya bi sawun Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya da ma al'ummar Nijeriya baki ɗaya wajen makokin jami'an rundunar waɗanda ajalinsu ya cim musu a bakin aiki. Buhari ya ce an soma gudanar da bincike domin gano sababin haɗarin, tare…
Read More
Haɗarin jirgin sama ya ci rai 7 a Abuja

Haɗarin jirgin sama ya ci rai 7 a Abuja

Daga AISHA ASAS Wani jirgin sama mallakar Rundunar Sojin Saman Nijeriya, mai lamba NAF 201 B350, ya yi haɗari a Abuja. Bayanai sun nuna lamarin ya faru ne da hantsin Lahadi bayan da jirgin ya samu matsalar inji inda ya yi haɗari garin sauka a Abuja. Sanarwar da ta fito daga Jami'in Haulɗa da Jama'a na Rundunar, Air Commodore Ibikunle Daramola, ta nuna tuni shugaban rundunar Air Vice Marshal IO Amao, ya bada umarnin gudanar da bincike kan lamarin. Baya ga tabbatar da aukuwar lamarin, Daramola ya sake tabbatar da cewa duka mutum 7 da ke cikin jirgin sun riga…
Read More
Ba za a biya diyya ba don kuɓutar da ɗaliban Kagara,  Minista Lai

Ba za a biya diyya ba don kuɓutar da ɗaliban Kagara, Minista Lai

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta ce babu wata diyya da za ta biya domin kuɓutar da ɗalibai da malaman sakandaren Kagara da aka yi garkuwa da su. Kazali, ta ce ba ta biya diyya ba wajen kuɓutar da ɗaliban Ƙanƙar da aka sace a jihar Katsina da kuma waɗanda aka kwashe a Dapchi, jihar Yobe. Ministan Larabarai da Raya Al’adu, Mr Lai Mohammed ne ya yi wannan bayani yayin tattaunawar da aka yi da shi a tashar talabijin ta Channels a safiyar Asabar, inda ya yi magana a kan ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen daƙile matsalar sace-sacen mutane…
Read More
Wanzar da zaman lafiya haƙƙi ne a kanku, cewar Hukumar Abuja ga sabbin jakadu

Wanzar da zaman lafiya haƙƙi ne a kanku, cewar Hukumar Abuja ga sabbin jakadu

Daga FATUHU MUSTAPHAMinistan Anuja, Malam Muhammad Musa Bello, ya yi kira ga sabbin jakadun Nijeriya da su kasance masu isar da saƙon zaman lafiya ga 'yan Nijeriya mazauna inda aka tura kowannensu. Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin jakadun a ofishinsa a matsayin wani ɓangare na cika sharuɗɗan matsayin da aka ba su. Da yake jawabi, Bello ya nusar da jakadun kan cewa Birnin Tarayya na nuni da haɗin kan da Nijeriya ke da shi ne, tare da tunatar da su taken bikin cikar Nijeriya shekara 60 da samun 'yancin kai da ya gabata…
Read More
Neja: Jerin sunayen waɗanda ‘yan bindiga suka sace a Kwalejin Kimiyya, Kagara

Neja: Jerin sunayen waɗanda ‘yan bindiga suka sace a Kwalejin Kimiyya, Kagara

Daga BASHIR ISAH A ranar 17/02/2021 wasu 'yan bindiga suka kai hari a Kwalejin Kimiyya ta Gwamnati da ke Kagara a yankin ƙaramar hukumar Rafi, jihar Neja, inda suka yi awon gaba da ɗalibai da malamai da sauransu. Manhaja ta yi ƙokarin tattaro sunayen waɗanda lamarin ya shafa, ga su kamar haka: Malamai da ma'aikata da sauransu; Hannatu PhilipLawal AbdullahiDodo FodioMohammed MusaFaiza MohammedChristiana AdamaFaith AdamaMaimuna SuleimanNura IsahAhmad IsahKhadizat IsahMohammed MohammedAisha IsahSaratu Isah . Ɗalibai; Jamilu IsahShem JoshuaAbbas AbdullahiIsah AbdullahiEzekeil DanladiHaliru ShuaibuMamuda SuleimanDanzakar DaudaAbdulsamad SanusiBashir AbbasSuleman LawalAbdullahi AdamuHabakuk AugustineIdris MohammedMusa AdamuAbdulkarim AbdulrahmanAbubakar DanjummaAbdullahi AbubakarBashir KamalideenMohammed SalisuYusuf M KabirIsah Abdullah MakusidiPolineous VicenteLawal…
Read More
NAFDAC ta gamsu da ingancin rigakafin AstraZeneca

NAFDAC ta gamsu da ingancin rigakafin AstraZeneca

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) ta ce, ta amince da ingancin maganin rigakafin korona na AstraZeneca don amfanin ƙasa. Shugabar hukumar, Mojisola Adeyeye ce ta sanar da hakan a wannan Alhamis. Da wannan, Nijeriya ta samu shiga jerin ƙasashen duniya da ke da dama wajen yaƙi da annobar korona. Yayin da take yi wa taron manema labarai bayani a Abuja, Adeyeye ta ce bayan da hukumar NAFDAC ta karɓi maganin, ba tare da ɓata lokaci ba ta sukunya bincike don tabbatar da ingancinsa. A cewar Adeyeye, baya ga rigakafin AstraZeneca da ta…
Read More
Nijeriya: An samu ƙaruwar matsalolin tsaro a ‘yan makonnin da suka gabata – Abdulsalami

Nijeriya: An samu ƙaruwar matsalolin tsaro a ‘yan makonnin da suka gabata – Abdulsalami

Daga FATUHU MUSTAPHA Tsohon Shugaban Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Zaman Lafiyar Ƙasa (NPC), General Abdulsalami Abubakar, ya ce a tsakanin makonni biyun da suka gabata matsalar rashin tsaro da rashin haɗin kai sun ƙaru a sassan Nijeriya. Don haka ya yi kira ga gwamnoni da su gyara ɗarama sannan su maganace waɗannan matsaloli da ke faruwa a jihohinsu. Abdulsalam ya yi kira ga 'yan ƙasa da a kasance masu haƙuri da juriyar mawuyacin halin da aka shiga, sannan a zamo masu sadaukarwa wajen daidaita lamurran ƙasa. Tsohon Shugaban Ƙasar ya yi wannan gargaɗi ne yayin ganawar da ya yi da…
Read More