Babban Labari

Buhari da Lawan sun nuna alhininsu kan haɗarin jirgi a Abuja

Buhari da Lawan sun nuna alhininsu kan haɗarin jirgi a Abuja

Daga AISHA ASAS Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa kan haɗarin jirgin saman sojoji da ya auku Lahadin da ta gabata a Abuja. Sanarwar da hadimin Buhari kan sha'anin yaɗa labarai, Femi Adesina ya fitar, ta nuna yadda Shugaba Buhari ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalai, 'yan'uwa da abokan aikin sojojin da suka rasu a haɗarin. Sanarwar ta ce Buhari ya bi sawun Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya da ma al'ummar Nijeriya baki ɗaya wajen makokin jami'an rundunar waɗanda ajalinsu ya cim musu a bakin aiki. Buhari ya ce an soma gudanar da bincike domin gano sababin haɗarin, tare…
Read More
Haɗarin jirgin sama ya ci rai 7 a Abuja

Haɗarin jirgin sama ya ci rai 7 a Abuja

Daga AISHA ASAS Wani jirgin sama mallakar Rundunar Sojin Saman Nijeriya, mai lamba NAF 201 B350, ya yi haɗari a Abuja. Bayanai sun nuna lamarin ya faru ne da hantsin Lahadi bayan da jirgin ya samu matsalar inji inda ya yi haɗari garin sauka a Abuja. Sanarwar da ta fito daga Jami'in Haulɗa da Jama'a na Rundunar, Air Commodore Ibikunle Daramola, ta nuna tuni shugaban rundunar Air Vice Marshal IO Amao, ya bada umarnin gudanar da bincike kan lamarin. Baya ga tabbatar da aukuwar lamarin, Daramola ya sake tabbatar da cewa duka mutum 7 da ke cikin jirgin sun riga…
Read More
Ba za a biya diyya ba don kuɓutar da ɗaliban Kagara,  Minista Lai

Ba za a biya diyya ba don kuɓutar da ɗaliban Kagara, Minista Lai

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta ce babu wata diyya da za ta biya domin kuɓutar da ɗalibai da malaman sakandaren Kagara da aka yi garkuwa da su. Kazali, ta ce ba ta biya diyya ba wajen kuɓutar da ɗaliban Ƙanƙar da aka sace a jihar Katsina da kuma waɗanda aka kwashe a Dapchi, jihar Yobe. Ministan Larabarai da Raya Al’adu, Mr Lai Mohammed ne ya yi wannan bayani yayin tattaunawar da aka yi da shi a tashar talabijin ta Channels a safiyar Asabar, inda ya yi magana a kan ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen daƙile matsalar sace-sacen mutane…
Read More
Wanzar da zaman lafiya haƙƙi ne a kanku, cewar Hukumar Abuja ga sabbin jakadu

Wanzar da zaman lafiya haƙƙi ne a kanku, cewar Hukumar Abuja ga sabbin jakadu

Daga FATUHU MUSTAPHAMinistan Anuja, Malam Muhammad Musa Bello, ya yi kira ga sabbin jakadun Nijeriya da su kasance masu isar da saƙon zaman lafiya ga 'yan Nijeriya mazauna inda aka tura kowannensu. Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin jakadun a ofishinsa a matsayin wani ɓangare na cika sharuɗɗan matsayin da aka ba su. Da yake jawabi, Bello ya nusar da jakadun kan cewa Birnin Tarayya na nuni da haɗin kan da Nijeriya ke da shi ne, tare da tunatar da su taken bikin cikar Nijeriya shekara 60 da samun 'yancin kai da ya gabata…
Read More
Neja: Jerin sunayen waɗanda ‘yan bindiga suka sace a Kwalejin Kimiyya, Kagara

Neja: Jerin sunayen waɗanda ‘yan bindiga suka sace a Kwalejin Kimiyya, Kagara

Daga BASHIR ISAH A ranar 17/02/2021 wasu 'yan bindiga suka kai hari a Kwalejin Kimiyya ta Gwamnati da ke Kagara a yankin ƙaramar hukumar Rafi, jihar Neja, inda suka yi awon gaba da ɗalibai da malamai da sauransu. Manhaja ta yi ƙokarin tattaro sunayen waɗanda lamarin ya shafa, ga su kamar haka: Malamai da ma'aikata da sauransu; Hannatu PhilipLawal AbdullahiDodo FodioMohammed MusaFaiza MohammedChristiana AdamaFaith AdamaMaimuna SuleimanNura IsahAhmad IsahKhadizat IsahMohammed MohammedAisha IsahSaratu Isah . Ɗalibai; Jamilu IsahShem JoshuaAbbas AbdullahiIsah AbdullahiEzekeil DanladiHaliru ShuaibuMamuda SuleimanDanzakar DaudaAbdulsamad SanusiBashir AbbasSuleman LawalAbdullahi AdamuHabakuk AugustineIdris MohammedMusa AdamuAbdulkarim AbdulrahmanAbubakar DanjummaAbdullahi AbubakarBashir KamalideenMohammed SalisuYusuf M KabirIsah Abdullah MakusidiPolineous VicenteLawal…
Read More
NAFDAC ta gamsu da ingancin rigakafin AstraZeneca

NAFDAC ta gamsu da ingancin rigakafin AstraZeneca

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) ta ce, ta amince da ingancin maganin rigakafin korona na AstraZeneca don amfanin ƙasa. Shugabar hukumar, Mojisola Adeyeye ce ta sanar da hakan a wannan Alhamis. Da wannan, Nijeriya ta samu shiga jerin ƙasashen duniya da ke da dama wajen yaƙi da annobar korona. Yayin da take yi wa taron manema labarai bayani a Abuja, Adeyeye ta ce bayan da hukumar NAFDAC ta karɓi maganin, ba tare da ɓata lokaci ba ta sukunya bincike don tabbatar da ingancinsa. A cewar Adeyeye, baya ga rigakafin AstraZeneca da ta…
Read More
Nijeriya: An samu ƙaruwar matsalolin tsaro a ‘yan makonnin da suka gabata – Abdulsalami

Nijeriya: An samu ƙaruwar matsalolin tsaro a ‘yan makonnin da suka gabata – Abdulsalami

Daga FATUHU MUSTAPHA Tsohon Shugaban Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Zaman Lafiyar Ƙasa (NPC), General Abdulsalami Abubakar, ya ce a tsakanin makonni biyun da suka gabata matsalar rashin tsaro da rashin haɗin kai sun ƙaru a sassan Nijeriya. Don haka ya yi kira ga gwamnoni da su gyara ɗarama sannan su maganace waɗannan matsaloli da ke faruwa a jihohinsu. Abdulsalam ya yi kira ga 'yan ƙasa da a kasance masu haƙuri da juriyar mawuyacin halin da aka shiga, sannan a zamo masu sadaukarwa wajen daidaita lamurran ƙasa. Tsohon Shugaban Ƙasar ya yi wannan gargaɗi ne yayin ganawar da ya yi da…
Read More
Bawa ya kama hanyar kafa tarihi a hukumar EFCC

Bawa ya kama hanyar kafa tarihi a hukumar EFCC

Daga FATUHU MUSTAPHA A halin da ake ciki, Abdulrasheed Bawa, ɗan shekara 40, ya kama hanyar kafa tarihi na zama mai mafi ƙarancin shekaru da zai shugabanci Hukumar Yaƙi da Zambar Kuɗaɗe da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa (EFCC). A ranar Talata Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa sunan matashin don neman amincewarta kan naɗa shi sabon shugaban EFCC. Bayanai sun nuna Bawa ƙwararre ne a fannin bincike dangane da batutuwan da suka shafi maguɗin kuɗi da sauran laifuka da suka danganci tattalin arziki. Tun bayan dakatar da shugaban riƙo na EFCC Ibrahim Magu, a ranar…
Read More
Kwamiti ya yi zaman farko don magance rashin zuwan yara makaranta

Kwamiti ya yi zaman farko don magance rashin zuwan yara makaranta

Daga FATUHU MUSTAPHA Kwamitin Gudanarwa kan Shirin Sabuwar Hanyar Bada Karatu (National Steering Committee on Alternate School Programme) ya yi taron sa na farko a ranar Litinin a Gidan Ma'aji (Treasury House) da ke Abuja. Taron ya fara aiwatar da tsare-tsare kan hanyoyin da za a bi a magance matsalolin da ke sanya yara su daina zuwa makaranta a Nijeriya tare da gaggauta rage yawan irin waɗannan yaran ta hanyar sama masu ilimin farko mai inganci da ilimin sana'o'in a wasu yanayi na musamman waɗanda ba a magance su a tsarin da ake da shi a yanzu ba. A jawabin…
Read More
‘Yan fashin daji na shirin mallakar makamai masu linzami, inji Sheikh Gumi

‘Yan fashin daji na shirin mallakar makamai masu linzami, inji Sheikh Gumi

Daga WAKILIN MU An bayyana cewa 'yan fashin daji da ke dazuzzakan jihohin Arewa suna shirin mallakar makaman kakkaɓo jirgin yaƙi domin daƙile hare-haren sojoji. Sheikh Abubakar Gumi ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da jaridar PUNCH ta yi da shi. A kwanankin baya ne Gumi ya ziyarci 'yan ta'addar a dajin Zamfara ya gana da su inda suka nuna suna satar mutane suna karɓar fansa ne domin tara kuɗaɗen sayen makamai. Bayan dawowarsa, Gumi ya yi kira ga gwamnati da ta duba ta yi wa ɓarayin afuwa domin ba su damar ajiye makamansu. Yayin ziyarar tasa Gumi ya…
Read More