Babban Labari

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

Daga AISHA ASAS Wasu 'yan bindiga sun kai hari a Tungan Maje da ke yankin Gwagwalada, Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mutum huɗu. Al'amarin wanda ya auku a tsakar daren wannan Lahadin, sai da 'yan bindigar suka shafe kimanin sa'o'i uku suna abin da suka ga dama a Tungan Maje kafin daga bisani suka yi awon gaba da wani tsohon jami'in Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) Abdulahi Idris Rakieu da wasu mutum biyu daga iyalan gidansa. A cewar jaridar TheCable, harin ya shafi wani mai suna Olusola Agun, wanda shi ya zama cikon na…
Read More
Amnesty International na neman wargaza Nijeriya – inji Lai Mohammed

Amnesty International na neman wargaza Nijeriya – inji Lai Mohammed

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Tarayya ta zargi Ƙungiyar Kare 'Yancin Ɗan-Adam ta Duniya (AI) da take-taken neman wargaza Nijeriya da gangar ta hanyar ɗora zarge-zarge a kan gwamnati da kuma sojoji. Ministan Labarai da Al'adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya yi wannan zargi yayin wata hira da wata tashar talabijin ta yi da shi a Juma'ar da ta gabata a Legas wadda Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) ta bibiya. Ministan ya bayyana haka ne a matsayin martani ga wani rahoton ƙungiyar a kan yaƙi da batun take 'yancin ɗan-Adam a faɗin duniya inda ta nuna an yi zargin an…
Read More
Buhari ya zaɓi tsoffin hafsoshi a matsayin jakadu

Buhari ya zaɓi tsoffin hafsoshi a matsayin jakadu

Daga WAKILIN MU Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa sunayen tsoffin hafsoshin tsaron da suka yi murabus kwanan nan, ga Majalisar Dattawa domin amincewa da naɗa su a matsayin jakadu. A cikin wasiƙar da Buhari ya aika wa Sugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, Buhari ya ce, "Bisa la'akari da Kundin Tsarin Mulki sashe na 171 (1) da sashe na (2) (c) da ƙaramin sashe na (4) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 na Tarayyar Nijeriya wanda aka yi wa gyaran fuska, ina mai gabatar da waɗannan sunaye guda 5 don neman amincewar Majalisar Dattawa kan yi musu naɗin…
Read More
Gwamnati ta amince da batun buɗe sabbin jami’o’i 20 a faɗin ƙasa

Gwamnati ta amince da batun buɗe sabbin jami’o’i 20 a faɗin ƙasa

Daga AISHA ASAS Majalisar Zartarwa ta Tarayya, ta aminta da batun samar da sabbin jami'o'i masu zaman kansu guda 20 a faɗin ƙasa. Majalisar ta cim ma wannan matsaya ne yayin zamanta na Larabar da ta gabata ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu ya ce, jami'o'in za su samu lasisin zarafin gudanarwa ne daga hannun Hukumar Kula da Jami'o'i ta Ƙasa (NUC), wanda za su yi amfani da shi nan da shekaru uku masu zuwa, yayin da gwamnati za ta ci gaba da sanya musu ido. Jami'o'in da Majalisar ta amince da a kafa ɗin…
Read More
Rasuwar Momoh: Na rasa babban amini – inji Buhari

Rasuwar Momoh: Na rasa babban amini – inji Buhari

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa dangane da rasuwar amininsa Prince Tony Momoh. A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya fitar a Litinin da ta gabata a Abuja, Shugaba Buhari ya bayyana cewa, marigayin ya kasance tare da shi a duk faɗi-tashin da ya sha. Yana mai cewa, "Samun kwatankwacin marigayin wajen biyayya a fagen siyasa, abu ne mai wahalar gaske. Zan yi rashin sa matuƙa." Jaridar Manhaja ta kalato Buhari ya yi tuna baya inda ya ce, "Marigayi Momoh ya ba da gagarumar gudunmawa a matsayinsa na Shugaban Sashen Yaɗa…
Read More
Sadarwa: Gwamnati ta tsawaita wa’adin shirin haɗe layukan sadarwa da lambar NIN

Sadarwa: Gwamnati ta tsawaita wa’adin shirin haɗe layukan sadarwa da lambar NIN

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta ƙara wa'adin shirin haɗe Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa da layukan sadarwa da makonni 8 domin bai wa 'yan ƙasa isasshen lokaci don su sada layukan sadarwarsu da lambar NIN. Sabon wa'adin da gwamnatin ta tsayar yanzu, shi ne zuwa ranar 6 ga Afrilu mai zuwa. Daraktan Hulɗa da Jama'a na Hukumar Sadarwa ta Ƙasa, Dr Ikechukwu Adinde, shi ne ya ba da bayanin haka a ranar Talata. Inda ya ce, Ministan Sadarwa Isa Pantami ne ya ba da umarnin tsawaita wa'adin bayan taron kwamitin sanya ido kan shirin haɗe lambar NIN da layukana sadarwa.…
Read More
Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Rashawa: SERAP ta buƙaci a binciki ɓacewar biliyan N4.4 a Majalisar Tarayya

Ƙungiyar Kare 'Yancin Zamantakewa Da Yaƙi Da Cin Hanci (SERAP), ta yi kira ga Shugaban Majalisar Dattawa Dr Ahmad Lawan, da takwaransa na Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Femi Gbajabiamila, a kan su buƙaci hukumomin yaƙi da rashawa su binciki badaƙalar ɓatan dabon da kasafin biliyan N4.4 na Majalisar Tarayya ya yi kamar yadda rahotannin binciken ofishin Babban Jami'in Bincike na Ƙasa suka nuna. A wata wasiƙa da ta samu sa hannun mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ƙungiyar ta ce, "Ta hanyar kwatanta jagoranci nagari a kan wannan batu, Majalisar Tarayya za ta iya nuna wa 'yan Nijeriya cewa ɓangaren yin…
Read More
Yaƙi Da Matsalar Tsaro: Zulum ya ƙalubalanci shugabannin tsaro su kyautata alaƙa da takwarorinsu

Yaƙi Da Matsalar Tsaro: Zulum ya ƙalubalanci shugabannin tsaro su kyautata alaƙa da takwarorinsu

Daga AISHA ASAS Gwamnan Jihar Barno, Babagana Umara Zulum, ya ƙalubalanci sabbin shugabannin tsaro da su assasa kyakkyawar alaƙar aiki a tsakaninsu da ƙasashen da Nijeriya ke maƙwabtaka da su, wato Chadi da Kamaru da kuma Nijar. Kazalika, ya shawarci manyan hafsoshin da su kasance masu haƙuri da kuma sauraron jama'a a halin aiwatar da ayyukansu. Gwaman ya faɗa wa jami'an haka ne sa'ilin da ya karɓi baƙuncinsu a fadar gwamnatin jihar a Lahadin da ta gabata yayin da suka yi ziyarar aiki ta farko a jihar. Shugaban tsaro Major-General Leo Irabor, shi ne ya jagoranci takwarorinsa Major-General Ibrahim Attahiru…
Read More
Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama a APC

Daga FATUHU MUSTAPHA A ranar Asabar da ta gabata Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sabunta rijistarsa ta zama cikakken dan jam'iyyarsu ta APC, a mahaifarsa Daura da ke jihar Katsina. Tare da kira ga daukacin shugabannin jam'iyyar da karfafa kwazo wajen tabbatar da APC ta samu karin tagomashi a matakin farko. Buhari ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karbi bakuncin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Lawan da wasu gwamnoni hada da wasu 'ya'yan jam'iyyar APC a garin Daura, jim kadan bayan ya kammala sabunta rijistarsa ta jam'iyya a Gundumar Sarkin Yara. A wata sanarwa da mai magana…
Read More
Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Rattaba wa dokar NOUN hannu da na yi ya haifar wa dalibanta samun tagomashi – Buhari

Daga AISHA ASAS Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, rattaba hannu da ya yi a dokar Budaddiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN) da aka yi wa gyaran fuska, ya haifar wa jami'ar da ɗalibanta samun tagomashi a kasa. Shugaban ya bayyana haka ne yayin bikin yaye daliban jami'ar karo na 9 da na 10 da aka hade wuri guda wanda ya gudana ta bidiyo a ranar Asabar da ta gabata. Da yake jawabi yayin bikin ta bakin wakilinsa Mataimakin Sakataren Hukumar Kula da Jami'o'i ta Kasa, Ramon Yusuf, Buhari ya ce, "Budaddiyar Jami'ar tana sauke nauyin da ya rataya a kanta…
Read More