Babban Labari

Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Cutar Korona: Za a tabbatar da kiyaye dokokin kariya a Abuja – Minista

Daga WAKILINMU Hukumar Birnin Tarayya, Abuja ta ce, za ta tabbatar da an bi dokokin yaki da Cutar Korona na 2021 kamar yadda Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da Cutar Korona ya shimfida. Hukumar ta bayyana haka ne a wajen wani taron masu fada a ji da ya gudana a karkashin jagorancin Ministan Abuja, Malam Muhammad Musa Bello, a Juma'ar da ta gabata a Abuja. Da yake jawabi yayin taron, Ministan Abuja ya ce, "Za a kara himma wajen wayar da kan mazauna Abuja game da kiyaye dokokin yaki da Cutar Korona, tare da tabbatar da an hukunta duk wanda…
Read More
Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Cutar Korona: Mutum 27 sun mutu a tsakanin sa’o’i 24 a Nijeriya

Daga UMAR M. GOMBE Cibiyar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ta bayyana cewa, an samu rasuwar mutum 27 cikin sa'o'i 24 a fadin kasa sakamakon Cutar Korona. Cibiyar ta sanar da hakan ne a shafinta na intanet a Juma'ar da ta gabata, inda ta ce kawo yanzu adadin wadanda suka mutu a fadin kasa a dalilin korona ya cilla zuwa mutum 1,557. Kazalika, NCDC ta sanar an samu karin mutum 1,114 da suka harbu da cutar ta korona a fadin kasa. Wanda a cewarta, "Ya zuwa yanzu mutum 128,674 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a fadin kasa."…
Read More
Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Majalisa na sane da nadin sabbin shugabannin hafsoshin da Buhari ya yi – Fadar Shugaban Kasa

Adaga FATUHU MUSTAPHA Fadar Shugaban Kasa ta sanar cewa sabbin shugabannin sojojin da aka nada kwanan nan za su bayyana gaban Majalisar Dattawa domin tabbatar da nadin nasu. A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a, Hadimin Shugaba Buhari Kan Harkokin Majalisar Tarayya (Bangaren Dattawa), Sanata Babajide Omoworare ya bayyana cewa, tuni Shugaba Buhari ya tura wasika ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, yana mai bukatar a tabbatar da nadin wadanda lamarin ya shafa. Sanarwar ta nuna cewa: “Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da Majalisar Tarayya nadin da ya yi tare da neman majalisar ta tabbatar da nadin nasa…
Read More
Kiris ya rage Obasanjo ya yi mini ritaya daga aiki – Buratai

Kiris ya rage Obasanjo ya yi mini ritaya daga aiki – Buratai

Daga UMAR M. GOMBE Tsohon shugaban rundunar sojan Nijeriya, Lt. Gen. Tukur Buratai, ya bayyana cewa, kiris ya rage tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya yi masa ritaya daga aikin soja shekaru 21 da suka gabata. Ya ce, wannan ya faru ne a lokacin yana matsayin Manjo, tare da bayyana samun zarafin kaiwa matsayin 'Lieutenant General' da kuma Babban Hafsan Hafsoshi da ya yi a matsayin al'amari da ya shiga tarihi. Buratai, ya yi wadannan bayanan ne yayin da yake jawabin bankwana wajen mika ragamar aiki ga magajinsa Maj. Gen. Ibrahim Attahiru a babban ofishin sojoji da ke Abuja a…
Read More
Inganta fannin lafiya shi ya fi muhimmanci ga Nijeriya bisa ga sayo rigakafin korona – Gates

Inganta fannin lafiya shi ya fi muhimmanci ga Nijeriya bisa ga sayo rigakafin korona – Gates

Daga FATUHU MUSTAPHA Hamshakin dan kasuwar nan na Kasar Amurka, Bill Gates, ya shawarci Nijeriya da ta karkatar da hankalinta zuwa ga inganta fannin lafiyarta maimakon kashe makudan kudade wajen sayo allurar rigakafin cutar korona. Gates ya ba da shawar ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai ta bidiyo a Talatar da ta gabata, inda ya yi kira ga Nijeriya da kada ta yi amfani da 'yan kudaden da ta ware don kula da fannin lafiyarta wajen sayen rigakafin COVID-19 mai tsadar gaske. Jaridar Manhaja ta kalato dan kasuwar na cewa, “Ina mai bada shawarar a bai wa…
Read More
Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Daga AISHA ASAS, Abuja Gwamnatin Tarayya ta ce, ana sa ran a soma allurar rigakafin cutar korona ya zuwa karshen Maris ko Afrilun 2021.Ministan Lafiya, Osagie Ehanire ne ya bayyana haka sa'ilin da Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da COVID-19 (PTF) ke gabatar da bayanin ayyukankasa, Litinin da ta gabata a Abuja. Ehanire ya ce, "Adadin maganin da Nijeriya ta yi odar sa ta AVATT na Hukumar Hada Kan Afirka, ya danganci daidai adadin da ake bukata ne don gundun barna." Ya ci gaba da cewa, Nijeriya na yin dukkan maiyiwuwa don tabbatar da an yi wa akalla kashi 70…
Read More
Cutar korona: NOA ta bukaci ‘yan Nijeriya su ba da hadin kai game da allurar riga-kafin korona

Cutar korona: NOA ta bukaci ‘yan Nijeriya su ba da hadin kai game da allurar riga-kafin korona

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Wayar da Kan 'Yan Kasa ta yi kira ga 'yan Nijeriya da su daina yarda da ra'ayoyi mara tushe da ake yadawa dangane da allurar riga-kafin cutar korona kan cewa maganin na tattare da wasu illoli.  Babban Daraktan hukumar, Garba Abari ne ya yi wannan kira a lokacin bayanin kore zargin da wasu ke yi cewa ana so a yi amfani da allurar ne wajen takaita yawan al'umma, lamarin da Abari ya ce ba gaskiya ba ne. Yana mai cewa, "Babu wata allurar riga-kafin da za a bari a shigo da ita Nijeriya ko a yi…
Read More
Kotu ta dage shari’ar El-Zakzaky zuwa 8 ga Maris

Kotu ta dage shari’ar El-Zakzaky zuwa 8 ga Maris

Kotu ta dage shri'ar El-Zakzaky zuwa 8 ga watan Maris Daga AISHA ASAS A Talatar da ta gabata babbar Kotun Jihar Kaduna da ke shari'ar jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya Ibrahim El-Zakzaky da matarsa  Zeenat, ta dage ci gaba da shari'ar ya zuwa ranar 8 da 9 ga watan Maris mai zuwa. Kotun ta dage shari'ar ne biyo bayan hukuncin da Alkali Gideon Kurada ya yanke dangane da neman kotu ta ba shi lokaci da lauyan El-Zakzaky Mr Femi Falana ya yi a bisa wakilcin Mr Eddie Inegedu, domin ba shi damar nazarin wani bidiyo da wasu shaidu biyu suka…
Read More
Tsaro: Shugaba Buhari ya nada sabbin hafsoshi

Tsaro: Shugaba Buhari ya nada sabbin hafsoshi

Daga Umar Gombe Bayanan da jaridar Manhaja ta samu daga Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, sun nuna Shugaba Muhammadu Buhari ya nada sabbin hafsoshin sojin Nijeriya. Wadanda nadin ya shafa su ne; Major General Leo Irabor a matsayin babban hafsan tsaron kasa da Maj. Gen. I Attairu a matsayin babban hafsan sojojin kasa, sai A Z Gambo a matsayin babban hafsan sojojin ruwa da kuma AVM IO Alao a msatsayin babban hafsan sojojin Sama. Kafin wannan lokaci, 'yan Nijeriya da dama sun yi ta bayyana ra'ayoyinsu kan bukatar da ke akwai na yi wa shugabannin sojoji garambawul don inganta…
Read More
“Filayen Nijeriya mallakar jihohi ne ba na Fulani ba” – Sanata Jibrin

“Filayen Nijeriya mallakar jihohi ne ba na Fulani ba” – Sanata Jibrin

Daga Fatuhu Mustapha An yi kira ga al'umar Fulani a fadin Nijeriya da su rungumi zaman lafiya da sauran kabilu tare da bai wa gwamnatocin jihohi hadin kai wajen yaki da ta'addanci. Sarkin Fulanin jihar Nasarawa kuma jigo a jam'iyyar PDP, Sanata Walid Jibrin ne ya yi wannan kira a wata sanarwa da ya fitar yau Talata. Jaridar Manhaja ta ruwaito Sanata Jibrin na cewa, "Ba na tare da duk wanda ke ra'ayin Fulani ne ke da mallakar filayen Nijeriya. Jihohi su ke da mallakar filaye." Sarkin Fulanin ya yi kira ga 'yan Nijeriya, musamman gwamnoin Ondo da Oyo da…
Read More