Siyasa

APC ta yi Allah wadai da harin da aka kai sakatariyarta a Zamfara

APC ta yi Allah wadai da harin da aka kai sakatariyarta a Zamfara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar APC reshen Zamfara ta yi Allah-wadai da harin da masu zanga-zanga suka kai sakatariyar jam’iyyar ta jihar. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar APC na jihar, Yusuf Idris ya fitar a Gusau ranar Litinin. Sanarwar tace jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta yi Allah-wadai da harin da wasu bata-gari da suka kai hari a yayin da ake gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa. "Ko a ranar juma’ar da ta gabata, jam'iyyar APC ta gargadi gwamnatin jihar kan yadda ta bar wasu bata gari suna huce haushin su kan…
Read More
Tallafin taki da Sanata Barau ya raba a Kano zai taimaka wajen bunƙasa noma – Hon. Yaƙub Takai

Tallafin taki da Sanata Barau ya raba a Kano zai taimaka wajen bunƙasa noma – Hon. Yaƙub Takai

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana irin tallafin taki ga manoma kyauta da mataimakin shugaban majalisar dattijai, Sanatan Kano ta Arewa Dakta Barau I Jibrin yake bayarwa ga dukkan ƙananan hukumomi 44 na jihar Kano da cewa zai mutuƙar taimakawa wajen bunƙasa noma a daminar bana. Hon. Yaƙub Husaini Takai ɗaya daga cikin manyan mataimaka na musamman ga mataimakin shugaban majalisar dattijai na ƙasa Sanata Barau I jibrin ne ya bayyana hakan da yake zantawa da 'yan jarida. Ya ƙara da cewa tsarin bayar da takin da Sanatan Kano ta Arewa ya kawo jihar Kano da aka ƙaddamar da…
Read More
 Za mu canja tsarin tafiyarmu ta siyasa a Jihar Katsina – Musa Bature

 Za mu canja tsarin tafiyarmu ta siyasa a Jihar Katsina – Musa Bature

Daga DAUDA USMAN a Legas Wani matashi kuma jigo a tafiyar siyasar jam'iyyar NNPP a Jihar Katsina, Alhaji Musa Bature Bakori dake cikin Jihar Katsina, ya jagoranci gudanar da taron neman haɗin kawunan tsofaffin shuwagabannin Jam'iyyar ta NNPP da sauran 'ya'yanta na shiyyar Funtuwa da kewayenta gaba ɗaya. Taron wanda ya samu halartar dukkan tsofaffin shuwagabannin jam'iyyar ta NNPP a shiyyar Funtuwa ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin Alhaji Musa Bature Bakori a ranar Asabar ɗin makon jiya. Alhaji Musa Bature Bakori ya ce sun yi gangamin kiran wannan taro ne domin tattaunawa a bisa kan rashin ingantaccen shugabanci tare…
Read More
PDP ta dakatar da Suswam da wasu ‘yan jam’iyya a Benuwai

PDP ta dakatar da Suswam da wasu ‘yan jam’iyya a Benuwai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP a Jihar Benuwai ta dakatar da Sanata Gabriel Suswam da Terngu Tsegba da Richard Gbande da Terseer Tsumba da Farfesa Nicholas Ada daga jam’iyyar. Haka kuma ta dakatar da shugabannin jam’iyyar na ƙananan hukumomin Apa, Gboko, Gwer-East, Katsina-Ala, Konshisha, Logo, Otukpo da Ukum. A ranar Laraba ne dai jam’iyyar ta gayyaci waɗanda abin ya shafa, bisa zarginsu da aikata zagon-ƙasa da kuma cin amanar jam’iyyar. Sammacin wanda ya nuna rashin jituwar da ke faruwa a cikin jam’iyyar a jihar, ya biyo bayan wani hari da wasu ɓatagari suka kai a sakatariyar jam’iyyar…
Read More
Sanata Ndume ya ba jami’iyyar APC haƙuri a kan sukar gwamnatin Tinubu

Sanata Ndume ya ba jami’iyyar APC haƙuri a kan sukar gwamnatin Tinubu

Tsohon bulaliyan Majalisar Dattijai, Sanata Ali Ndume ya ba shugabancin jam'iyyar APC mai mulki haƙuri saboda rashin tuntuɓar jam'iyyar kafin yayi zargin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da rashin kyakkyawan shugabanci. Ndume wanda ke wakiltar Kudancin Borno a majalisar dattijai, duk da haka ya ce yana nan kan bakarsa, yana jaddada cewa duk abin da ya faɗa ko ya aikata ya fito ne daga kishin ƙasa. "Jiya jam’iyya ta gayyace ni kuma ga ni a nan don mu tattauna abubuwa game da abin da ya faru wanda kowa ya sani, haƙiƙa shugaban jam’iyya ba wai kawai shugaban jam’iyya bane a…
Read More
Sanatan Zamfara ya raba taki ga manoma 3,000

Sanatan Zamfara ya raba taki ga manoma 3,000

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Sanata Sahabi Ya’u mai wakiltar mazaɓar Zamfara ta Arewa ya sayo tirela huɗu na takin zamani ga manoma dubu uku a mazaɓarsa. Sanata Sahabi Ya'u yayin da yake ƙaddamar da rabon takin a garin ƙaura Namoda, hedkwatar ƙaramar hukumar ƙaura Namoda a ranar Lahadin da ta gabata, ya bayyana cewa takin da ya samar kyauta ne. A cewarsa kowace ƙaramar hukumar ƙaura Namoda, Shinkafi, Birnin Magaji da Zurmi domin amfana da babbar mota ɗaya. Ya ci gaba da cewa, za a raba buhunan taki iri-iri guda 500 ga manoma marasa galihu yayin da za a…
Read More
An yi zanga-zangar goyon bayan Tinubu a Kano

An yi zanga-zangar goyon bayan Tinubu a Kano

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Masu zanga-zangar goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu sun fito kan tituna a Jihar Kano. Masu wannan zanga-zanga suna yin ta ne a daidai lokacin da Nijeriya ta ɗauki zafi da zanga-zangar nuna adawa da halin yunwa da tsadar rayuwa a ƙasar. Masu wannan zanga-zanga sun fito ne ta titin Audu Baƙo da kuma Farm Centre suna bayyana adawa ga abin da suka kira zanga-zangar tashin hankali. Sun kuma yi taro a Fadar Sarkin Kano da ke Nasarawa, inda suka saurari jawabai kan hanyoyin da za a magance matsalolin da ke addabar ƙasar. Da…
Read More
Zan yi aiki da Wike idan ya nemi gafarata – Sanata Kingibe

Zan yi aiki da Wike idan ya nemi gafarata – Sanata Kingibe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sanata mai wakiltar babban birnin tarayya, FCT, Ireti Kingibe, ta bayyana aniyar yin aiki da ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, idan har zai ba ta haƙuri kan kalaman ɓatanci da aka yi mata. Ku tuna cewa Mrs Kingiɓe da ministar sun samu saɓani a kan salon shugabanci a FCT. A ranar 1 ga watan Yuli, Mista Wike ya yi barazanar tsige Sanatan a zaɓen 2027 idan ta ci gaba da sukar shugabancinsa a babban birnin tarayya Abuja. Har ma ya tambaye ta ta "je ki rungume taransfoma" idan ba ta gamsu da shi…
Read More
‘Yan siyasar baya na shekaru 16 ne ke da alhakin matsalar Arewa – Uba Sani

‘Yan siyasar baya na shekaru 16 ne ke da alhakin matsalar Arewa – Uba Sani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya ce ‘yan siyasa da suka yi mulki a shekaru 16 da suka gabata ciki har da shi su ne ke da alhakin matsalolin da suka dabaibaye Arewa. Ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gaji rugujewar tsari daga gwamnatin da ta shuɗe. Gwamna Uba Sani wanda ya kasance babban baƙo na musamman a wajen taron bunƙasa ɗalibai wanda babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin ɗalibai ya shirya mai taken “Student-Centric Goɓernance: Bikin cika kwanaki 365 na shugabancin Sanata Uba Sani mai tasiri”, ya ce masu…
Read More
Zanga-zanga: PDP a Zamfara ta musanta ɗaukar nauyin kai hari gidajen Matawalle da Sahabi

Zanga-zanga: PDP a Zamfara ta musanta ɗaukar nauyin kai hari gidajen Matawalle da Sahabi

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jam’iyyar PDP reshen Jihar Zamfara dake mulki a jihar ta musanta zargin da jam'iyyar APC tayi na ɗaukar nauyin ‘yan bangar siyasa da suka yi yunƙurin Kai hari gidan tsohon gwamna kuma ministan tsaro na jihar, Hon Bello Muhammad Matawalle da ke Gusau da kuma fasa rumbun ajiya mallakin Sanata Sahabi Ya'u a garin Kaura Namoda a yayin gudanar da zanga-zanga da aka yi ranar Alhamis a faɗin ƙasar. Muƙaddashin shugaban jam'iyyar na jiha kuma shugaban ma'aikatan gwamna Dauda Lawal, Hon. Muktar Lugga ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai…
Read More