31
Oct
Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar a Abuja ya buƙaci ɗaukacin 'yan Nijeriya da su yi amfani da damar da jam’iyyar PDP ta bayar wajen daidaita Nijeriya da ceto ƙasar daga halin da ta ke ciki. Atiku ya ba da wannan cajin ne ga wakilai da jami'an jam'iyyar a babban taron jam'iyyar PDP na 2021. A cewarsa, akwai bambance-bambance da dama, amma 'yan Nijeriya za su iya cimma komai idan suka ajiye saɓanin da ke tsakaninsu a gefe. Ya ƙara da cewa, taron wata dama ce ta yanke…
