Mata A Yau

Kwalliya ce jarin ‘ya mace – Hauwa Ibrahim

Kwalliya ce jarin ‘ya mace – Hauwa Ibrahim

“Tun ban fi shekara 18 ba na fara aikin gwagwarmaya"  Daga AISHA ASAS A yanzu dai kai ya waye, kusan na ce birni da ƙauye mun aminta mace mai sana'a ita ce mace, wadda ba ta yi kuwa ta rako su ne. Muhimmancin sana'a ga 'ya mace ba zai misaltu ba, hakan ya sanya a kullum ake faɗa tare da janyo hankalin mata kan neman na kai. A wannan satin filin mata a yau ya yi wa masu karatu babban kamu, inda mu ka ɗauko maku ɗaya daga cikin matan da su ka cancanci a kirasu da Gimbiya saboda jajircewa…
Read More
Ko a tarbiyya za a gane ‘ya’yan mace mai ilmi – Dakta Erisa Danladi

Ko a tarbiyya za a gane ‘ya’yan mace mai ilmi – Dakta Erisa Danladi

"Ina cikin mata masu ƙananan shekaru da suka yi fice a duniya"  Daga ABUBAKAR A. BOLARI, a Gombe Dakta Erisa Sarki Danladi, Babbar manomiya ce kuma yar gwagwarmaya a ɓangaren ayyukan raya karkara, kuma mai fafutuka tsakanin ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba wato NGO's. Mace mai ƙoƙarin taimakon marasa galihu. Gatan marar gata. Ita ce babbar daraktar ƙungiyar nan mai suna 'Motherhen Deɓelopment Foundation', da ta ke koyawa mata da matasa sana’o'in hannu, sannan kuma ko-odinata ce ta Arewa maso Gabas ta wata ƙungiyar tallafa wa mata 'yan siyasa wato 'women in political empowerment', da sauran ƙungiyoyi da dama…
Read More
Ku bar mata su nemi na kansu – Jiddah Nguru 

Ku bar mata su nemi na kansu – Jiddah Nguru 

“A wannan zamani kusan dole ne neman na kai ga ’ya mace” Daga AISHA ASAS  Kalmar neman na kai ga 'ya mace na da ma'anoni da dama a tsakanin al'umma, musamman a ƙasar Hausa. Yayin da ka ce, ku ƙyale 'ya'ya mata su nemi na kansu, wasu kan fassara hakan da ku bar mata su lalace, ko su ba wa mata dama su zama kamar maza, ko kuma su bar mata su yi yadda suke so. Wasu kuma sai suke ganin kamar hanya ce ta yaɗa manufofin Yahudu.  Wannan na ɗaya daga cikin dalilan da suke sa wasu mazan tirjiya…
Read More
Akwai buƙatar dawo wa da sarakuna ƙarfin mulkin da suke da shi a baya – Gimbiya Umma Usman Nagoggo

Akwai buƙatar dawo wa da sarakuna ƙarfin mulkin da suke da shi a baya – Gimbiya Umma Usman Nagoggo

"Mata ba su da wata rawa da suke takawa a masarautun ƙasar Hausa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Shafin Gimbiya na wannan makon ya lalubo muku Gimbiya ce ta gaske, domin kuwa tana daga cikin ýaýa 42 da tsohon Sarkin Katsina marigayi Usman Nagoggo ya haifa, wato Hajiya Umma Hassan, ýar uwa ga marigayi Janar Hassan Usman Katsina, tsohon Gwamnan tsohuwar Jihar Arewa. Gimbiya ýar sarki, matar sarki, kuma uwar sarki, wacce ta shafe tsawon shekaru tana hidima ga al'umma da taimakon raunana, kuma mamba a Jam'iyyar Matan Arewa. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu, Gimbiya Umma Hassan…
Read More
Chayilo: Yarinyar da mijin mahaifiyarta ya maida tamkar kuyangar sa

Chayilo: Yarinyar da mijin mahaifiyarta ya maida tamkar kuyangar sa

"Chayilo ta sanar da mahaifiyar ta abinda mijinta ke yi mata, amma ta hauta da faɗa" Daga COMFORT MUKOLLO a Gombe  Shafin Gimbiya na wannan mako ya yi waiwaye kan yadda cin zarafin 'ya'ya mata ya yawaita musamman a Arewacin Nijeriya, inda yara ƙanane da ma manya ke fuskantar barazanar cin zarafi, abin takaici kaso mai yawa daga cikinsu makusantansu ne ke keta masu haddi. Da wannan ne shafin namu ya yi ɗamarar bada gudunmawa ta hanyar wallafa rahotannin da bayyanai da ka iya taimako ko ƙwato haƙƙin waɗanda aka ci zarafinsu, ko bada kariya ga waɗanda ba su faɗa…
Read More
Ta yaya za ki kula da fatarki a lokacin sanyi

Ta yaya za ki kula da fatarki a lokacin sanyi

Daga AISHA ASAS  Yayin da aka ce sanyi ya ƙarato, mutane da yawa suna tausayawa halin da fatarsu za ta shiga yayin da suka yi arangama da yanayin na sanyi. A lokacin sanyi fata na yamushewa saboda yanayin iskar hunturu, kuma yakan yi muni musamman ga waɗanda ba su san yadda za su ba wa fatar tallafi ba. Yanayin sanyi ba iya fata ya tsaya ba, domin hunturu na taɓa lafiyar gashi, ta hanyar yawan karyewa, sai kuma uwa uba kaushi ko fasau da ƙafa ke yi. Waɗannan matsalolin na lokacin sanyi na sauya fasalin jiki tare da sanya shi…
Read More
Rayuwar mata bayan mutuwar miji

Rayuwar mata bayan mutuwar miji

Daga AISHA ASAS Akwai bambanci sosai tsakanin wadda aka saki da wadda mijin ya mutu - Sa'adatu Kankia  “Ta hanyar gina matanku ne kawai za ku samun tabbacin ‘ya’yanku ba za su tagayyara bayan mutuwarku” Kamar yadda aka sani, shafin Gimbiya na jaridar Blueprint Manhaja bai tsaya a iya tattaunawa da mata kan rayuwarsu ba. Shafin kan taɓo matsaloli, cigaba da kuma wani abu da ke ciwa mata tuwo a ƙwarya, don tattaunawa da kuma nema masu mafita. A yau shafin zai yi duba kan halin da mata ke shiga bayan mutuwar mazajensu, wanda ba kasafai ake fahimtar halin da…
Read More
Karatun ‘ya’ya mata ne mafita ga taɓarɓarewar tarbiyya – Hajiya Fati Jajere

Karatun ‘ya’ya mata ne mafita ga taɓarɓarewar tarbiyya – Hajiya Fati Jajere

iyaye ku daidaita tsakanin karatun 'ya'ya maza da mata Daga ABUBAKAR A BOLARI, Gombe Hajiya Fati Isa Jajere, ita ce shugabar gidauniyar F-Jajere Foudation, 'yar Kasuwa ce kuma ‘yar siyasa, sannan kuma basarakiya. A tattaunawar da wakilinmu Abubakar A. Bolari, ya yi da ita, ta bayyana tarihin rayuwarta da kuma irin nasarori da ta samu. Ga yadda tataunawar ta kasance; MANHAJA: Hajiya za mu so jin taƙaitacen tarihinki. HAJIYA FATI: Sunana Fati Isa Jajere, ni ‘yar asalin garin Jajere ce a ƙaramar Hukumar Fune a Jihar Yobe, Arewa maso-gabas a tarayyar Nijeriya. Mahaifina Bafulatanin Jajere ne, mahaifiyata kuma Bahaushiya ce…
Read More
Ta hanyar haɗa kai ne ‘yan siyasa mata za su samu ‘yancinsu – Fatima Kadashi

Ta hanyar haɗa kai ne ‘yan siyasa mata za su samu ‘yancinsu – Fatima Kadashi

"Faɗuwa a siyasa ma nasara ce" Daga AISHA ASAS Sanannen abu ne mata a wannan zamani sun yunƙuro kan sha'anin siyasa, sun kuma nuna za su iya idan aka ba su dama ta ɓangaren riƙe madafun iko a ƙasar nan. Sai dai hakan ya zama wata barazana ga wasu mazan 'yan siyasa ganin cewa idan suka yi wasa hula za ta bi bayan ɗankwali ne a harkar siyasar Nijeriya. Wannan tunanin na su ne ya sa suke amfani da ƙarfin ikonsu wurin ganin sun hana mata kataɓus a fagen siyasa, ta hanyar danne su, su hana su motsi, har su…
Read More
An bar Arewa a baya ta fuskar samun damar karatu kyauta – Dakta Habiba Iliyasu 

An bar Arewa a baya ta fuskar samun damar karatu kyauta – Dakta Habiba Iliyasu 

Al'umma ta fi amfana da ilimin mace fiye da namiji Daga ABUBAKAR M. TAHEER  Dakta Habiba Iliyasu Atta wadda senior lakcara ce a Department ɗin Microbiology na Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zariya. A cikin wannan tattaunawa da wakilinmu Abubakar M Taheer ya yi da ita, ta kawo matsalolin dake saka ƴan Arewa rasa damar samun guraben karatu a ƙasashen waje. Haka kuma Dakta ta kawo irin nasarorin da ta samu wajen samun 'scholarship' na PTDF da hanyoyin da mutum zai bi wajen samun irin damar da ta samu, wato 'scholarship' ɗin, tare kuma da bayyana mana irin ƙalubalai da…
Read More