Mata A Yau

Ni ce na yi ta ɗaya a gasar harbi da aka yi a Katsina  – Jamila Sharp Shooter 

Ni ce na yi ta ɗaya a gasar harbi da aka yi a Katsina  – Jamila Sharp Shooter 

"Har yanzu aljanu na zo min a barci don gaya min abinda zai faru"  Daga UMAR AKILU MAJERI  Jamila Adamu Gombe 'yar mafarauta ce da ta yi fice akan harkar tsaro a Hukumar tsaro ta civil defense wadda hukumar take alfahari da ita wajan iya sarrafa bindiga. Hajiya Jamila, ta taɓa samun lambar yabo akan ƙwarewar harbi a lokacin da ta je samun wani horo na sanin makamar aiki a Jihar Katsina a lokacin da ta halarci horon ƙwarewa akan harbi da aka shiryawa ma'aikatan hukumar su 205 a lokacin ita kaɗai ce mace a cikinsu kuma ita ce ta…
Read More
Bayan mutuwar aurena na fara sana’ar awara domin ɗaukar nauyin ‘ya’yana – Fatima Isma’il 

Bayan mutuwar aurena na fara sana’ar awara domin ɗaukar nauyin ‘ya’yana – Fatima Isma’il 

"Rashin kulawar mijina ga 'ya'yana bai sare min gwiwa wurin ba su ilimi ba" Daga UMAR AKILU MAJERI  Hajiya Fatima Isma'il Abbas wata mata ce da ta yi fice akan sana'ar yin kosai, awara da kwai da kuma kunun tsamiya da koko wadda ta fara yin wannan sana'ar ta awara tun kimanin shekaru goma sha biyar da suka gabata.  Hajiya Fatima wadda aka fi sani da Hajiya Magajiya ýar asalin garin Gumel da take zaune a unguwar Zai, kuma take yin sana'arta a kusa da ofishin NEPA a Dutse. A tattaunawar ta da Manhaja, ta shawarci mata su zama masu…
Read More
Babu dalilin da zai sa iyaye yi wa ‘ya’yansu auren dole – Jamila Rijiyar Lemo

Babu dalilin da zai sa iyaye yi wa ‘ya’yansu auren dole – Jamila Rijiyar Lemo

Auren dole kan iya sa mace ta kashe mijinta - Lantana Jafar  Daga AISHA ASAS  A wannan satin shafin Gimbiya ya karɓi baƙuncin mata guda biyu, waɗanda suka kasance fitattu kan sha’anin bayar da gudunmuwa a ɓangaren tarbiyya da kuma zamantakewar aure.  Dalilin gayyatar tasu dai ba ɓoyayye ba ne, kasancewar shafin namu na duba ne kawai ga buƙatun uwayen gida, hanyoyin da za su bi kan gyara zamantakewar su ta aure ko zaman gida, zuga ga tarbiyyar 'ya'yansu da kuma zaburarwa kan neman na kai. Baƙin namu za su amsa mana tambayoyi ne kan ɗaya daga cikin matsalolin da…
Read More
Ban taɓa sanin wani abu kishi ba sai bayan mutuwar mijina – Zainab Garba Fago 

Ban taɓa sanin wani abu kishi ba sai bayan mutuwar mijina – Zainab Garba Fago 

"Na jima ban samu miji ba saboda suna zargin ina ɗauke da ciwon da ya kashe mijina" Daga UMAR AKILU MAJERI  Hajia Zainab Garba Fago matashiya ce mai ƙoƙarin neman na kanta domin ta rufa wa kanta da kanta asiri, mace ce mai kamar maza wadda ta jima tana yin gwagwarmaya domin ganin ta rufawa kanta asiri.  Zainab wadda ýar asalin ƙabilar itiloce da ke Jihar Binue a kudancin Nijeriya kuma mahaifiyarta bafillatana ce daga yankin Masarautar Hadejia acan ƙaramar Hukumar Guri. Za mu iya cewa, Hajiya Zainab ruwa biyu ce duk da cewar mahaifinta ɗan ƙabilar Itilone ita kuma…
Read More
Mafi yawan mutuwar aure laifin mata ne – Hussaina Shafi’u

Mafi yawan mutuwar aure laifin mata ne – Hussaina Shafi’u

"Na san wahalar da mata marasa miji suke fuskanta" "Sana'ar mafifi ce sana’ar da na dogara da ita" Daga UMAR AKILU MAJERI  Hussaina tana ɗaya daga cikin matasan mata a yankin ƙaramar Hukumar Kiyawa da ta yi fice wajan yin saƙa musamman saƙar mafici wadda ake yin amfani da shi wajan yin fifita a gidajan masu hannu da shuni. Hajiya Hussaina ba ta tsaya iyanan ba malama ce da take da ilimin addini, ga haƙuri, ga kuma sanin darajar mutane. Ba ta da saurin fushi ga karamci wajan girmama al'umma. Wakilinmu na Jihar Jigawa Umar Akilu Majeri shi ne wanda…
Read More
Lauyoyi mata na ba wa mata gudunmawa mai yawa a kotu – Barista Mariya

Lauyoyi mata na ba wa mata gudunmawa mai yawa a kotu – Barista Mariya

"Mu na bayar da gudunmawa wajen kare haƙƙin mata ba tare da karɓar kuɗi ba" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Aikin lauya aiki ne na kare haƙƙoƙin jama'a a gaban shari'a, don ƙwatowa mai haƙƙi haƙƙinsa da tabbatar da ganin an yi wa wanda aka zalunta adalci, an kuma hukunta wanda ya yi ba daidai ba. Ga duk ma'aboci bibiyar yadda ake gudanar da shari'a ko ganin yadda lauyoyi ke muhawara da bincike don kare wanda suke wakilta, ya san cewa, aikin ba ƙarami ba ne, aiki ne da ke buƙatar jajircewa, nuna rashin tsoro da kuma dagewa a kan gaskiya.…
Read More
 Ba laifi ko rashin so ke sa maza ƙarin aure ba – Sa’adatu Kankia 

 Ba laifi ko rashin so ke sa maza ƙarin aure ba – Sa’adatu Kankia 

Yana daga cikin matsalar maza wofuntar da matansu idan za su ƙara aure - Likitar Ma'aurata  Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da sake ganin zagayowar sati lafiya, kuma sannunku da jimirin bibiyar jaridar Blueprint Manhaja. A wannan satin kamar yadda mukan yi a wasu lokuta mun tattauna kan ɗaya daga cikin ababen da ke ci wa ma'araurata tuwo a kwarya, wato matsalolin da ke tasowa yayin ƙarin aure. Domin kawo maku gamsashen bayani, mun gayyato maku sanannun mata da suka jima suna bayar da gudunmuwa a zamantakewar aure, wato Sa’adatu Saminu Kankia, da kuma Zuwaira Kolo, wadda ku ka…
Read More
Mun sha zama da majalisar dokoki kan ilimin mata – Nafisa Halliru

Mun sha zama da majalisar dokoki kan ilimin mata – Nafisa Halliru

"Tun 2012 zuwa yau nake ba wa gwamnatin Jigawa gudunmawa wajan cigaban ilimi" Daga UMAR AKILU MAJERE Hajiya Nafisa Halliru Haruna wata fitacciyar ýar gwagwarmayar ƙungiyoyi ce da sunanta ya jima a harkar Jihar Jigawa akan harkokin ilimi da kiwon lafiya. Hajiya Nafisa tana ɗaya daga cikin mata da suka sadaukar da rayuwarsu domin cigaban al'umma musamman wajan ganin ta sanya 'ya'ya mata sun shiga andama wajan samun ilimin boko da na zamani. Nasani mai karatu zai so ya ji tarihin hajiya Nafisa da jin asalinta ko daga ina ta fito? Hajiya Nafisa Halliru an haife ta a garin Birnin…
Read More
Ni ke yi wa mijina komai duk da cewa ina aiki – Hannatu Muhammed

Ni ke yi wa mijina komai duk da cewa ina aiki – Hannatu Muhammed

"Ba addinin da ya bai wa mata gata kamar Musulunci" "Duk wadda za ta zuga ki ki yi wa mijinki rashin kunya ba mai son ki ba ce" (Ci gaba daga makon jiya) Daga UMAR GARBA a Katsina  A satin da ya gabata, mun faro tattaunawa da jajirtacciyar 'yar jarida, kuma shugabar ƙungiyar mata 'yan jarida ta Jihar Katsina, wato NAWOJ. A tattaunawar mun taɓo ɓangarori da dama, wanda muka yada zango a tambayar da muka yi alƙawarin kawo maku amsarta kafin wasu su biyo baya. Har wa yau dai, wakilinmu a Katsina, Umar Garba ne ke jan ragamar tattaunawar.…
Read More
Ko namiji aka ci zarafinsa za mu tsaya ma shi – Hannatu Muhammed 

Ko namiji aka ci zarafinsa za mu tsaya ma shi – Hannatu Muhammed 

"Dalilin shugabancina mata sun samu 'yanci a Katsina" Daga UMAR GARBA a Katsina Hajiya Hannatu Muhammed ita ce Shugabar ƙungiyar Mata 'Yan Jarida Reshen Jihar Katsina, wato NAWOJ, a halin yanzu ita ce mataimakiyar babban manja na gidan talabijin na ƙasa, wato NTA da ke Katsina, ta yi fice a fannoni da dama kama daga gabatar da shirye shirye a gidan talabijin, bai wa mata shawara game da yadda zasu kyautata zamantakewa da iyalansu. Kazalika fitacciyar 'yar jaridar ta kasance 'yar gwagwarmaya da ke wayar da kan mata don su fuskanci ƙalubalen rayuwa da ke gabansu. Wakilin Manhaja a Katsina…
Read More