Mata A Yau

Ina da kishin ganin mata sun samu ilimi da sana’a – Fatima Abdullahi 

Ina da kishin ganin mata sun samu ilimi da sana’a – Fatima Abdullahi 

"Ranar Hijabi ta Duniya ba ta Musulmai kaɗai ba ce" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Hajiya Fatima Suleiman Abdullahi ba ɓoyayyiya ba ce a garin Jos da wasu sassan Jihar Filato, inda ta shafe tsawon shekaru tana gudanar da ayyukan jinƙai da taimakawa al'umma, faɗakarwa da kuma sasanta tsakanin ma'aurata. Mace ce mai kishin ganin mata sun samu ilimi da sana'a, don su dogara da kansu. Duk da kasancewar ta babbar ma'aikaciyar gwamnati, amma aikinta bai hana ta shiga ƙauyuka da lunguna daban-daban ba, domin ta gana da raunanan mata da waɗanda rikice-rikice suka raba da mahallansu. Wakilin Blueprint Manhaja, Abba…
Read More
Haɗa iyali da aikin gwamnati da kuma sana’a da wahala sosai – Khadija Batsari 

Haɗa iyali da aikin gwamnati da kuma sana’a da wahala sosai – Khadija Batsari 

"Matasa a dage a nemi sana'a a daina ɓata data ga banza" Daga UMAR GARBA, a Katsina  Khadija Nura Batsari da aka fi sani da Umnoorthrifts, ma'aikaciyar gwamnati ce kuma matashiyar 'yar kasuwa da ke amfani da shafukan sada zumunta don bunƙasa harkokin kasuwancinta. Wakilin Blueprint Manhaja a Katsina Umar Garba, ya tattauna da Khadija Umnoorthrifts game da batutuwan da suka shafi dabarun tallata kasuwanci a kafofin sada zumunta, ba wa matasa maza da mata shawara a kan su dogaro da kansu don su zamo masu amfani ga al'umma, nasarori da kuma ƙalubalen da ta fuskanta kafin ta taka matakin…
Read More
Duk takalmin da aka kawo zan iya yin irinsa har ma a kasa gane bambanci – Kadeeja Ahmad

Duk takalmin da aka kawo zan iya yin irinsa har ma a kasa gane bambanci – Kadeeja Ahmad

“Na yi ƙwarewar da zan iya gane ingancin takalma kowanne iri ne” Daga AISHA ASAS A yau shafin Mata A Yau ya ɗauko wa masu karatu matashiyar da ta zama allon kwaikwayo ga kowacce mace da ta san ciwon kanta, babba ko ƙarama, domin ta ce wa matasan mata idan ba ku yi, to, ku ba ni wuri, kuma ta tabbatar wa mata cewa, ba sana’ar da mace ba zata iya yi ba ko ta fi ƙarfinta, domin ta ɗauko ɗaya daga cikin sana’o’in da suka yi tambari da sunan jinsin maza, wato sana’ar ƙera takalma, inda ta koya, ta…
Read More
Nazari: Ku gina matanku ku na raye, su gina ‘ya’yanku bayan mutuwarku

Nazari: Ku gina matanku ku na raye, su gina ‘ya’yanku bayan mutuwarku

Daga AISHA ASAS “Ta hanyar gina matanku ne kawai za ku samu tabbacin ‘ya’yanku ba za su tagayyara ba bayan mutuwarku” Kamar yadda aka sani, shafin Mata A Yau na sashen Gimbiya a jaridarku ta Blueprint Manhaja bai tsaya a iya tattaunawa da mata kan rayuwarsu ba. Shafin kan taɓo matsaloli, cigaba da kuma wani abu da ke ciwa mata tuwo a ƙwarya, don tattaunawa da kuma nema masu mafita. A yau shafin zai yi duba kan halin da mata ke shiga bayan mutuwar mazajensu, wanda ba kasafai ake fahimtar halin da suke shiga ba. Ita mace rayuwarta gabaɗayanta a…
Read More
 Babu sana’ar da ke kawo min kuɗi kamar ta sabulai – Hauwa Dashiru

 Babu sana’ar da ke kawo min kuɗi kamar ta sabulai – Hauwa Dashiru

"Ban samu karɓuwa ba sai lokacin da gwamnati ta kafa dokar hana yawo lokacin Buhari " Daga UMAR AKILU MAJERI  Hajiya Hauwa Dashiru Muhd wata Hajiya ce a cikin mata a Jihar Jigawa da ta yi suna wajan gyaran jiki musamman yadda ake wa mata masu shirin amarcewa gyaran fata. Hajiya Hauwa ta shahara a wannan daɓe na yi wa amare dilka, gyaran gashi, turaren mata da tiraren jiki da haɗa humra da nufin kyautata dangantaka tsakanin amarya da ango a gidajen aure. Wakilinmu na Jihar Jigawa ya samu tattaunawa da Hajiya Hauwa Dashiru akan yadda takeyiwa amare gyaran jiki…
Read More
Har yanzu mata ba sa samun cikakken ‘yanci da mutuntawa – Hauwa Babaji 

Har yanzu mata ba sa samun cikakken ‘yanci da mutuntawa – Hauwa Babaji 

"Zama mace dama ce ta zama gwarzuwa kuma jajirttacciya" (Ci gaba daga makon jiya) Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  MANHAJA: Waɗanne nasarori ki ka cimma kawo yanzu? HAUWA: Alhamdulillah, duk da ƙananan shekaruna, akwai wasu manyan nasarori da Allah ya ba ni damar cimmawa a wannan tafiya. Na fara daga ƙanana ne, amma yanzu ni ce Kwamishiniya ta jiha, a ƙungiyar Nigerian Girl Guides Association a Gombe, inda nake jagorantar shirye-shirye da dama da suka shafi yara mata a fannoni daban-daban kamar wayar da kai kan jinin al’ada.  Na kafa tawa ƙungiyar, wato Teens Care Foundation. Na yi aiki da manyan…
Read More
Na sha ganin yara mata na wulaƙanta saboda jinin al’ada – Hauwa Musa Babaji 

Na sha ganin yara mata na wulaƙanta saboda jinin al’ada – Hauwa Musa Babaji 

"Iyaye su ba wa 'ya'yansu mata murya, su saurare su" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Hauwa Musa Babaji matashiya ce ýar gwagwarmaya, malamar makaranta, kuma ýar kasuwa, wacce ke zaune a garin Gombe. Ita ce shugabar ƙungiyar Teens Care Foundation, wacce ke tallafawa rayuwar yara mata da suka fara shiga shekarun balaga. Tana gudanar da ayyuka da dama na wayar da kai, da suka haɗa ba da shawarwari ga ýammata kan yadda za su tunkari ƙalubalen rayuwa, ta fuskar ilimi, lafiya, tsafta, da mu'amalarsu da yara maza. Wakilin Blueprint Manhaja, Abba Abubakar Yakubu, ya tattauna da ita game da yadda take…
Read More
Sai ki na da kuɗi za ki inganta tarbiyyar ’ya’yanki – Salamatu Ringim

Sai ki na da kuɗi za ki inganta tarbiyyar ’ya’yanki – Salamatu Ringim

"Sana'ar yajin daddawa sana'a ce mai matuƙar riba" Daga UMAR AKILU MAJERI, a Dutse Hajiya Salamatu Abdullahi wata mace ce da ta yi fice a kan harkar noman kaji da kiwon awaki ayankin ƙaramar Hukumar Ringim, baya ga wannan, ta kasance tana aiki a ma'aikatar ilimi ɓangaran kula da makarantun sakandire, fannin kula da nagartar ilimi. Wakilinmu na Jihar Jigawa Umar Akilu Majeri, ya samu zantawa da Hajiya Salamatu akan hanyoyin da za su taimaka wajan inganta tarbiyyar yara ƙanana tare da matakan da za a ɗauka wajan magance matsalar da yake haddasa yawan mace-macen aure musamman a Arewacin Nijeriya.…
Read More
Duk wata ƙungiya da take son cigaba dole sai ta haɗa kai da gwamnati – Balaraba Abdullahi 

Duk wata ƙungiya da take son cigaba dole sai ta haɗa kai da gwamnati – Balaraba Abdullahi 

"Yin amfani da tsumma lokacin al'ada na iya haifarwa mace matsala" Daga UMAR AKILU MAJERI  Hajiya Balaraba Abdullahi ita ce Shugabar ƙungiyar Ayman Care ta Jihar Jigawa kuna Shugabar ƙungiyar mata manoma, wato Women in Agric Bussine reshen Jihar Jigawa ta tofa albarkacin bakinta akan yadda kiwon shanu da raguna ke kawo wa mata kuɗi. Hajiya Balaraba ta faɗi kaɗan daga cikin alfanon kiwo da yadda idan mata za su yi za su anfana kuma kiwon zai taimaka wajan magance zaman banza a tsakanin al'umma . Wakilinmu na Jihar Jigawa Umar Akilu Majeri ya samu zantawa da Hajiya Balaraba akan…
Read More
Ni ce na yi ta ɗaya a gasar harbi da aka yi a Katsina  – Jamila Sharp Shooter 

Ni ce na yi ta ɗaya a gasar harbi da aka yi a Katsina  – Jamila Sharp Shooter 

"Har yanzu aljanu na zo min a barci don gaya min abinda zai faru"  Daga UMAR AKILU MAJERI  Jamila Adamu Gombe 'yar mafarauta ce da ta yi fice akan harkar tsaro a Hukumar tsaro ta civil defense wadda hukumar take alfahari da ita wajan iya sarrafa bindiga. Hajiya Jamila, ta taɓa samun lambar yabo akan ƙwarewar harbi a lokacin da ta je samun wani horo na sanin makamar aiki a Jihar Katsina a lokacin da ta halarci horon ƙwarewa akan harbi da aka shiryawa ma'aikatan hukumar su 205 a lokacin ita kaɗai ce mace a cikinsu kuma ita ce ta…
Read More