05
Dec
Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ƙungiyoyin mata a ko'ina a faɗin duniya, na gudanar da wani gangamin wayar da kan al'umma game da yaƙi da cin zarafin mata da tauye musu haƙƙoƙin su a fuskar shari'a, shugabanci, siyasa, da zamantakewa. Wannan gangami na tsawon kwanaki 16 wanda ake yi wa laƙabi da Orange the World a Turance, yana mayar da hankali ne wajen tattauna yadda za a kawo ƙarshen wasu matsaloli 16 da manyan mata da ƙananan yara mata ke fuskanta a cikin al’ummomi daban-daban na duniya. Gangamin na so ne a kawo ƙarshen wulaƙanta mata a gidajen aure. A…