12
Aug
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Makomar Neymar idan har ya rabu da PSG na cigaba da kasancewa cikin rashin tabbas a daidai lokacin da ɗan wasan tare da ƙungiyar ta sa suka amince da Shirin rabuwar nan ba da jimawa ba. Sai dai mai yiwuwa burin ƙungiyoyin Barcelona da Chelsea waɗanda ke son ƙulla yarjejeniya da ɗan wasan ya gaza cika, saboda ƙalubalen da kowannensu ke fuskanta. A ɓangaren Chelsea, a yayin da ta kasance ƙungiyar da za fi dacewa da samun sauƙin sayen Neymar, ba lallai bane ɗan wasan ya amince da tayin komawa gare ta, la’akari da cewar ba…
