15
Jul
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) ta haramta wa Al-Nassr rajistar sabbin ’yan wasa saboda rashin biyan wasu kuɗaɗen da Leicester City ke bin ta a wani ɓangare na yarjejeniyar Ahmed Musa. Al-Nassr ya sayi Cristiano Ronaldo ne a watan Janairun 2023 amma FIFA ta dakatar da ita daga sake yin rajistar sabbin ’yan wasa sakamakon taqaddama ƙungiyar Leicester. Hakan ya faru ne sakamakon gazawar kulob ɗin Saudiyyar na kasa biyan ƙungiyar Leicester ƙarin kuɗaɗe dangane da yarjejeniyar da ta yi da ɗan wasan Nijeriya, Ahmad Musa. Tsohon ɗan wasan gaban CSKA Moscow ya koma Foxes…
