Shin akwai dalilin zaɓen APC a kakar zaɓen 2023?

Daga BELLO MUHAMMAD SHARAƊA

A shekara bakwai da watanni na mulkin Najeriya a karkashin tutar jam’iyyar APC:

  1. Ba su gyara wutar lantarki ba.
  2. Ba su gyara tsaron Rai ba.
  3. Ba su gyara tsaron dukiyar jama’a ba.
  4. Ba su gyara harkar lafiya da ilimi ba.
  5. Ba su gyara musibar rashawa ba.
    6.Ba su gyara tsadar abinci da kayan noma ba.
  6. Ba su gyara hauhawar farashin kayan masarufi ba.
  7. Ba su gyara darajar Naira da tashin Dala ba.
  8. Ba su gyara hanyoyin sufurin sama da qasa da ruwa ba.
  9. Ba su gyara aikin gwamnati ba a kowanne mataki
  10. Sun yi alƙawurra ba su cika ba. An ba su amana sun ci. A duk zancen da za su yi sai sun yi ƙarya.
  11. A jihohin Arewa da kudu, guda 36 har da Abuja
    37, an zavi APC a jiha 26 a shekarar 2015. A yanzu akwai gwamnonin APC a jiha 24, amma babu jihar da ba a kuka da mulkin APC.
  12. Babu jihar da APC bata dagula lissafin jama’a ba.
  13. Babu jihar da mutanen jihar ba su yi Allah wadarai da gwamnatin APC ba.

A zaɓen shekarar 2023 APC sai an bata wuta! Idan ta gama shan wuta, sai kore ta daga kan mulki.

Bello Muhammad Sharaɗa, masani ne kuma mai sharhi a kan al’amurran siyasa. Ya rubuto daga jihar Kano.