Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Daga BASHIR ISAH

Ya zuwa ranar Litinin ta makon gobe idan Allah Ya kai mu ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa da ya naɗa.

Sanarwar da ta fito ta bakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ta ce bikin rantsarwa zai gudana ne a babban zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da misalin ƙarfe 10 na safe.

Sanarwar ta ƙara da cewa ‘yan rakiya biyu-biyu kacal aka amince wa ministocin su take musu baya zuwa wajen taron.

“Ana sa ran ministocin kowanne ya zo da ‘yan rikiya guda biyu.

“Sannan duka ministocin da sauran baƙi kowa ya kasance a mazauninsa da misalin ƙarfe tara na safe,” in sanarwar.

Waɗanda za a rantsar ɗin sun haɗa da:

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani – Bosun Tijani

Ƙaramin Ministan Muhalli – Ishak Salaco

Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki – Wale Edun

Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki – Bunmi Tunji

Ministan Lantarki – Adedayo Adelabu

Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al’umma – Tunji Alausa

Ministan Ma’adinai – Dele Alake

Ministan Yawon Buɗe-Ido – Lola Ade-John

Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola

Ministan Kasuwanci da Zuba Jari – Doris Anite

Ministan Wasanni – John Enoh

Ministan Abuja – Nyesom Wike

Ministar Al’adu – Hannatu Musawa

Ministan Tsaro – Muhammad Badaru

Ƙaramin Ministan Tsaro – Bello Matawalle

Ƙaramin Ministan Ilimi – Yusuf T. Sununu

Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Ahmed M. Dangiwa

Ƙaramin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Abdullah T. Gwarzo

Ministan Kasafi da Tsare-Tsare – Atiku Bagudu

Ministan Muhalli (Kaduna)

Ƙaramar Ministar Abuja – Mairiga Mahmud

Ministan Albarkatun Ruwa – Bello M. Goronyo

Ministan Noma da Samar da Abinci – Abubakar Kyari

Ministan Ilimi – Tahir Maman

Ministan Harkokin Cikin Gida – Sa’Idu A. Alkali

Ministan Harkokin Waje – Yusuf M. Tuggar

Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a – Ali Pate

Ministan Harkokin ‘Yan Sanda – Ibrahim Geidam

Ƙaramin Ministan Ƙarafa – U. Maigari Ahmadu

Ministan Ƙarafa – Shuaibu A. Audu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai – Muhammed Idris Malagi

Ministan Shari’a – Lateef Fagbemi

Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Simon B. Lalong

Ƙaramar Ministar Harkokin Cikin Gida – Imaan Sulaiman-Ibrahim

Ministan Ayyuka na Musamman – Zephaniah Jisalo

Ministan Albarkatun Ruwa – Joseph Utsev

Ƙaramin Ministan Noma da Samar da Abinci – Aliyu Sabi Abdullahi