Editor

9513 Posts
Tinubu ya yi ganawar sirri da Ganduje da jiga-jigan APC na Kano

Tinubu ya yi ganawar sirri da Ganduje da jiga-jigan APC na Kano

Saga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi ganawar sirri da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje. Ganduje ya jagoranci wata tawaga da ta kunshi shugabannin jam’iyyar APC reshen Jihar Kano domin ganawa da Tinubu a fadar shugaban qasa ta Aso Rock Villa da ke Abuja, ranar Alhamis. Taron na ranar Alhamis ya zo ne mako guda bayan da Kotun Koli ta yanke hukuncin amincewa da Abba Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin halastaccen zababben gwamnan jihar da korar karar dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna. A watan Maris din da ya gabata ne dai mulki ya…
Read More
Gwamna Inuwa ya kai labari a Kotun Ƙoli

Gwamna Inuwa ya kai labari a Kotun Ƙoli

Daga BASHIR ISAH Kotun Ƙoli a ranar Juma'a ta tabbatar wa Gwamnan Jihar Gombe, Inuwa Yahaya, nasarar da ya samu a zaben 2023. Kotun ta yanke hukuncin haka ne bayan da ta yi watsi da karar da dan takarar jam'iyyar PDP a zaben na ran 18 ga Maris, 2023, Mohammed Barde ya daukaka inda yake kalubalantar nasarar da Inuwa ya samu. Barde ya daukaka kara ne kan cewa zaben da ya bai wa inuwa nasara cike yake sa badakalar sayen kuri'u. Sai dai baki daya shari'o'in da aka yi kan zaben a kotuna matakai uku, sun tabbatar da Inuwa a…
Read More
Ibadan: Waɗanda suka mutu sun ƙaru zuwa biyar

Ibadan: Waɗanda suka mutu sun ƙaru zuwa biyar

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Adadin wadanda suka mutu sakamakon fashewar wani abu da ya afku a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, a ranar Talata, 16 ga watan Janairu, ya kai mutum biyar. A ranar Laraba da daddare, gwamnan jihar, Seyi Makinde, yayin da yake bayar da karin haske a gidan talabijin na Channels Television a wani shirin siyasa mai taken "Politics Today", ya ce an samu mutuwar mutane biyu a ranar Talata, inda ya qara da cewa wani wanda abin ya shafa ya mutu a asibiti ranar Laraba. Sai dai a wani sabon rahoto da aka fitar a…
Read More
Wasan farko na Maroko yana nuna karsashin ƙungiyar na lashe gasar AFCON – Rahoto

Wasan farko na Maroko yana nuna karsashin ƙungiyar na lashe gasar AFCON – Rahoto

Daga MAHDI M. MUHAMMAD kungiyar Kwallon Kafar Kasar Maroko da ta girgiza duniya a 2022 da ta kai wasan daf da na karshe a gasar kofin duniya, ta samu nasarar doke Tanzania da ci 3-0 a kan 'yan wasa 10 a ranar Laraba a gasar kofin nahiyar Afirka, wanda hakan ke nuna karsashin kungiyar na lashe gasar Kofin Nahiyar Afrika. Kyaftin Romain Saiss, Azzedine Ounahi da Youssef En-Nesyri duk sun ci wa Morocco kwallo a birnin San-Pedro da ke gabar tekun Ivory Coast, yayin da Tanzania ta kori Novatus Miroshi. Duk da cewa kasar Maroko ta kasance kasa mai karfin…
Read More
Tsaro: Gwamnan Zamfara ya haramta wa sarakunan gargajiya bada izinin haƙar ma’adina

Tsaro: Gwamnan Zamfara ya haramta wa sarakunan gargajiya bada izinin haƙar ma’adina

Daga BASHIR ISAH A matsayin mataki na ci gaba da yaki da matsalar tsaro a Jihar Zamfara, Gwamnan Jihar, Dauda Lawal, ya rattaba hannu kan dokar da ta haramta wa sarakunan gargajiya a fadin jihar bai wa masu hakar ma'adinai izinin gudanar da harkokinsu a jihar. Lawal ya ba da wannan umarnin ne yayin taron Majalisar Zartarwa na Jihar da ya gudana a Fadar Gwamnatin Jihar a ranar Alhamis. Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar ran Alhamis cewa, an ba da wannan umarni ne domin dakile matsalar 'yan fashin dajin…
Read More
Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci ta ƙara jaddada goyon bayanta ga Shugaba Tinubu

Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci ta ƙara jaddada goyon bayanta ga Shugaba Tinubu

Majalisar Kolin ta ce ta sami kwarin gwiwar jaddada goyon bayan nata ga Shugaban Kasa Bola Tinubu da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ne biyo bayan hukuncin da Kotun Kolin ta Nijeriya ta yanke kan raba gardamar zabe inda kotun ta tabbatar da Shugaba Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben na shekarar 2023. Majalisar ta ce hukuncin ya kara tabbatar da cewa zaben da majalisar ta yi ba na tumun-dare ba ne don ya dace da zabin 'yan kasa. A cikin wata sanarwa da Majalisar ta fitar a wajen taronta na kasa na yini biyu da aka gudanar a…
Read More
An kama ɗalibin Jami’ar Bauchi ya mallaki bindiga ba bisa ƙa’ida ba

An kama ɗalibin Jami’ar Bauchi ya mallaki bindiga ba bisa ƙa’ida ba

Daga BASHIR ISAH Jami'an tsaro a jihar Bauchi sun kama wani dalibin Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa University (ATBU) Bauchi bisa zargin mallakar bindiga ba bisa ka'ida ba. Kakakin Rundunar 'Yansandan Bauchi, Ahmed Wakil, ya bayyana a ranar Laraba cewa, an tsare dalibin ne a ranar Asabar da ta gabata bayan da 'yan bijilanti suka kwarmata musu cewa dalibin ya mallaki karamar bindiga kirar gida har da alburushi. Ya ce tuni dalibin wanda dan aji hudu ne a ATBU ya amsa laifin da ake zarginsa. Ya kara da cewa, wanda ake zargi ya yi ikirarin asali bindigar ta wani ce wanda…
Read More
Yadda ‘yan ta’adda suka kai hari a sansanin sojoji a Katsina

Yadda ‘yan ta’adda suka kai hari a sansanin sojoji a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Barayin daji fiye da mutum 100 kan babura dauke da muggan makamai sun kai hari a sansanin jami'an tsaro da ya kunshi sojoji da 'yan sanda, a sansanin dake garin Nahuta a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina. Majiyar Manhaja ta bayyana cewar, sojojin sun mayar da martani ta hanyar bude wa 'yan bindigar wuta amma barayin sun fi su yawa sun kuma shammace su lamarin da ya tilasta jam'in tsaron janye. Bayan shafe kimanin sa'o'i biyu da rabi bangarorin biyu na dauki ba dadi, barayin sun samu nasarar kone Kayayyakin hansanin jami'an tsaron da…
Read More