30
Dec
Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Kwamared Adam Abubakar Adam wanda aka fi sani da Jagora, daya daga cikin jagororin Kungiyoyin Ci Gaban Al'umma a Karamar Hukumar Nasarawa Jihar Kano ya yaba wa hazikin marubucin nan Malam Hamisu Ibrahim wanda ya bada gudunmawa wajen rubuta littafi wanda ya kunshi kalmomin Larabci zuwa Turanci domin amfanin masu son koyon Larabci tun daga tushe kamar dai yadda Jagoran ya bayyana cewa wannan ba karamin aiki ba ne da zai taimaka wa wadanda suka san Turanci su koyi Larabci a matakin farko. Jagora ya kara da cewa "akwai bukatar marubutanmu su yi amfani da…
