Editor

9513 Posts
Ya kamata gwamnatin tarayya ta haramta shigowa da tsofaffin motoci Nijeriya – (NADDC)

Ya kamata gwamnatin tarayya ta haramta shigowa da tsofaffin motoci Nijeriya – (NADDC)

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar tsarawa da kera motoci ta Nijeriya ta yi kira ga gwamnatin Tarayya a kan ta haramta shigo da tsofaffin motoci da aka yi amfani da su daga shekarar 2000 zuwa 2007 cikin Nijeriya. Jaridar Persecondnews ta rawaito cewa, bayanan da aka samu a binciken Hukumar kasuwancin Kasa da kasa a Amurka ta samar, ya bayyana cewa, bukatar ababen hawa/motoci a Nijeriya na kowacce shekara ta tasam ma guda 720,000 yayin da masana'antu na cikin gida suke iya samar da guda 14,000 kacal a kowacce shekara. Don haka ake shigo da ƙari wasu motocin don a…
Read More
Ƙungiyar Gwamnoni ta maka tsohon Daraktanta a kotu kan zarginta da almundahana

Ƙungiyar Gwamnoni ta maka tsohon Daraktanta a kotu kan zarginta da almundahana

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta musanta zargin karkatar da kudade da tsohon Daraktanta na Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Abdulrazaque Bello Barkindo, ya yi. News Point Nigeria ta rawaito cewa, cikin wata wasikar sirri da ya aike wa Gwamna AbdulRasaq, Barkindo ya fallasa cewa a halin da ake ciki NGF ta fi bai wa hada-hadar kudi muhimmanci fiye da ayyukan cigaba. Barkindo ya jaddada cewa, kungiyar ta zama wata kafa inda wasu tsiraru ke amfana da ita, don haka ya bukaci a gudanar da cikakken bincike kan yadda NGF ke tafiyar da kudadenta. Sai dai, a wata sanarwa da…
Read More
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa zai sanya baki don hana Shoprite barin Jihar Kano

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa zai sanya baki don hana Shoprite barin Jihar Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), zai sanya baki don dakatar da yunkurin da katafaren shagon hada-hadar kasuwanci na Shoprite ya dauka na rufe reshensa daya tilo a jihar Kano. Katafaren kantin sayar da kayayyakin dake Ado Bayero Mall a Kano, a makon da ya gabata sun sanar da matakin ficewa daga cibiyar kasuwanci a watan Janairun da zai kama, inda suka bayyana cewa hakan ya biyo bayan yanayi na kalubalen tattalin arziki da ake fuskanta. An samu ra'ayoyi daban-daban dangane da matakin da Shoprite ta dauka wadda ke aiki a jihar…
Read More
Ta yaya za ki kula da fatarki a lokacin sanyi

Ta yaya za ki kula da fatarki a lokacin sanyi

Daga AISHA ASAS Yayin da aka ce sanyi ya karato, mutane da yawa suna tausayawa halin da fatarsu za ta shiga yayin da suka yi arangama da yanayin na sanyi. A lokacin sanyi fata na yamushewa saboda yanayin iskar hunturu, kuma yakan yi muni musamman ga wadanda ba su san yadda za su ba wa fatar tallafi ba. Yanayin sanyi ba iya fata ya tsaya ba, domin hunturu na tava lafiyar gashi, ta hanyar yawan karyewa, sai kuma uwa uba kaushi ko fasau da kafa ke yi. Wadannan matsalolin na lokacin sanyi na sauya fasalin jiki tare da sanya shi…
Read More
Mutum 11 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa

Mutum 11 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa

Daga BASHIR ISAH Akalla mutum 11 ne aka rawaito sun riga mu gidan gaskiya a ranar Asabar da ta gabata sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da su a yankin Kwanar Gujungu da ke Karamar Hukumar Taura a Jihar Jigawa. Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Jigawa, ASP Lawan Shiisu, shi ne ya tabbatar da aukuwar hakan jiya Lahadi a Dutse, babban birnin jihar. Shiisu ya ce hatsarin ya auku ne a ranar Asabar da misalin karfe 12:00 na rana, inda wata mota kirar Honda saloon mai lamba NSR 469 AE da wata kirar Golf wagon mai dauke da lamba AUY…
Read More
Saƙon Kirsimeti: Mu haɗe kai mu yaƙi maƙiya cigaban ƙasa, kiran CDS ga ’yan Nijeriya

Saƙon Kirsimeti: Mu haɗe kai mu yaƙi maƙiya cigaban ƙasa, kiran CDS ga ’yan Nijeriya

Daga BASHIR ISAH An yi kira ga al’ummar Nijerya da su hade kai wajen yaki makiya cikgaban kasa a wannan lokuci na bukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara. Babban Hafsan Tsaron Kasa, Janar Christopher Musa ne ya yi wannan kira a cikin sakon taya murna da ya fitar a ranar Lahadi mai dauke da sa hannun Mukaddashin Daraktan Yada Larabai na rundunar soji, Birgediya Janar Tukur Gusau. “Yayin da muka bi sahun masu bikin Kirsimeti da sabuwar shekara a fadin duniya, ina yabo ga Sojojin Nijeriya da ’yan Nijeriya bisa jajircewarsu. Da fatan alherin da ke tattare da wannan lokaci ya…
Read More
Sarkin Kano ya ƙaddamar da kwamitin bikin shekara 90 da KOFA ta tsara yi a 2025

Sarkin Kano ya ƙaddamar da kwamitin bikin shekara 90 da KOFA ta tsara yi a 2025

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano          Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya kaddamar da kwamitin shirye-shiryen bikin cika shekara 90 da kafuwar makarantar firamare ta Kofar Kudu, wace aka kafa a 1935 a gidan Sarkin Kano wanda qungiyar tsofaffun dalibai wato Kofar Kudu Old Pupils Primary School, (KOFA) karkashin shugabancin Kwamared Abubakar Shehu Kwaru ke shirin aiwatarwa da bikin a 2025 idan Allah ya kaimu lafiya. Kamar dai yadda Sarkin Kano ya kaddamar da wannan kwamiti a lokacin taron kungiyar na shekara 50 da dalibai karkashin shugabancin Alhaji Yusuf Aliyu Yakasai,  ya aji na shekarar 1972 wanda…
Read More
Matatar Fatakwal za ta fara aiki bayan shekaru

Matatar Fatakwal za ta fara aiki bayan shekaru

*Tinubu ya bada umarni maido da tsarin ciyar da dalibai Daga MAHDI M. MUHAMMAD Matatar mai fetur ta Fatakwal da ke Jihar Ribas za ta sake fara aiki bisa alqawarin da Gwamnatin Tarayya ta yi na tabbatar da samar da tace kayan a cikin gida a watan Disamba na 2023. Cigaban yana zuwa ne bayan shekaru da yawa da rufe matarar da kuma gyara kayan aikinta. Uku daga cikin matatun mai na Nijeriya a Fatakwal, Warri da Kaduna su na da qarfin tace ganga 445,000 a kowace rana, amma an rufe su tun a shekarar 2019. Sai dai kuma a…
Read More
Za mu hukunta likitocin da ke safarar ƙoda a Nijeriya – Gwamnati

Za mu hukunta likitocin da ke safarar ƙoda a Nijeriya – Gwamnati

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Nijeriya ta bayar da tabbacin daukar mataki kan likitoci da sauran mutanen da ke da hannu a harkar safarar koda. Jami'ar yada labarai ta ma'aikatar lafiya ta kasar, Ms Patricia Deworitshe ce ta bayar da tabbacin cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba a Abuja, babban birnin Nijeriya. A cewar jami'ar, gwamnati ta sanar da kudirinta na ladabtar da duk wanda aka kama da hannu a safarar koda bayan rahoton da jaridar Daily Trust ta wallafa kan yadda ake yin harkar a boye. Ta ce "ma'aikatar ta yi tir da irin wannan…
Read More
Nigeria Air: Majalisa ta gayyaci tsohon Ministan Sufurin Jirage – Sirika

Nigeria Air: Majalisa ta gayyaci tsohon Ministan Sufurin Jirage – Sirika

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Wakilai ta umarci kwamitinta kan harkokin sufurin jiragen sama da ya gayyaci Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, domin ya yi ma ta bayanin halin da kamfanin dakon kaya na kasa, Nigeria Air, ke shirin yi, har zuwa lokacin da zai bar mulki. Ana sa ran tsohon ministan zai bayar da haske a kan batutuwa da dama da suka shafi aikin. Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da Hon. Tarkighir Dickson ya gabatar a zauren majalisar ranar Alhamis.Da yake gabatar da kudirin, ya ce tsohon ministan a shekarar 2016 ya ba da shawarar…
Read More