Editor

9513 Posts
An gudanar da taron ƙara wa juna sani don bunƙasa cigaban kiwon kifi a Kano

An gudanar da taron ƙara wa juna sani don bunƙasa cigaban kiwon kifi a Kano

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Ƙungiyar masu noman kifi na Nijeriya reshen jihar Kano "Practicing fish famers association of Nijeriya"ta gudanar da taron wayar da Kan manoman kifi da qaddamar da sabuwar kasuwar kifi a Kano. Shugaban kungiyar na Kano Alhaji Nura Uba Ramadan ya ce sabuwar Kasuwar ta zo da sabon tsari ba kamar na baya ba. Yanzu an daidaita farashin kifi bai daya da biyan kudi nan take da samar da Manhaja na saye da sayarwar kifi da kaiwa inda ake bukata. Ya koka da cewa yanzu harkar kiwon kifi ana samun koma baya ne,dan haka suka mai…
Read More
Za mu tabbatar da ɗa’a da bin doka a ƙungiyar Lore – Bilya Ubale

Za mu tabbatar da ɗa’a da bin doka a ƙungiyar Lore – Bilya Ubale

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano A ranar Talatar da ta gabata ne kungiyar Lore na masu sayar da babura da ke kasuwar ’yan babura a kan titin Murtala Muhammad ta gudanar da zaben sabbin shugabaninta. Zaben da Alhaji Bilya Ubale Muktar ne ya yi nasarar zama sabon shugaban kungiyar ta Lore da yawan quri'u 380 da aka kada hakan tasa ya sami nasara akan abokin takarar sa Alhaji Husaini M.Y.Abdullahi Fagge da ya sami kuri'u 128. A mukamin mataimakin shugaban kungiyar Ashiru Abubakar shine ya sami nasara ba tare da hamayya ba, haka ma sauran matakai na zaben na muqamai…
Read More
Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero ta zaɓi sababbin shugabanni

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero ta zaɓi sababbin shugabanni

Daga WAKILINMU A kokarin ganin sun ciyar da Jami'ar Bayero da ke Kano gaba, a ranar 16 ga watan Disambar nan na 2023 ne ƙungiyar tsofaffin daliban Jami'ar da suka ci moriyar ta suka zabi sababbin shugabannin da za su tafiyar da kungiyar. Kungiyar ta 'BUK Alumni Association BUKAA' ta zavi sababbin shugabannin n, inda aka zabi Alhaji Shu'aibu Idris Miqati a matsayin shugaba na kasa, wanda ya guda a harabar makarantar da ke Kano. Wadanda aka zaɓa ɗin su ne; Shugaba - Alhaji Shuaibu Idris Mikati Mataimakin shugaba na I - Aare Akinwumi Akinyemi Mataimakin shugaba na II -…
Read More
Kasafin 2024: Gwamna Lawal ya ware N1.3b don zamanatar da kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati

Kasafin 2024: Gwamna Lawal ya ware N1.3b don zamanatar da kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Zamfara ta ware Naira biliyan 1.3 a kasafinta na 2024 don zamananta kafafen yada labarai mallakar jihar. Kwamishinan Yada Labarai da Raya Al'adu na Jihar, Mannir Haidara, shi ne ya bayyana haka ranar Litinin a Gusau, babban birnin jihar, jim kadan bayan gabatar da kasafin ma'aikatarsa ga Kwamitin Kudi na Majalisar Dokokin jihar. Kwamishinan ya jaddada cewa zamanantar da kafofin yada labarai mallakar jihar ya yi daidai da kudurin Gwamna Lawal na farfado da masana'antar yada labarai ta jihar. Ya kara da cewa, Kamar yadda aka sani, ma'aikatar ke da alhakin yada labarai a fadin…
Read More
An yi janazar mutane takwas da ‘yan bindiga suka hallaka a Katsina

An yi janazar mutane takwas da ‘yan bindiga suka hallaka a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Wata dabar 'yan ta'adda dauke da muggan makamai sun bude wa 'yan kasuwa takwas wuta, kusa da kauyen babangida bayan da suka dawo cin kasuwar Jibiya dake karamar hukumar Jibiya a jihar Katsina. Kakakin rundunar 'yan sanda a jihar ya tabbatar da faruwar lamarin. 'yan ta'addar sun kuma jikkata wasu karin mutane hudu a yayin da wasu biyu suka bata tun bayan harin da aka kai jiya Lahadi da dare. Wadanda aka kashe din mazauna kauyen 'Yan gayya ne a karamar hukumar ta Jibiya dake makota da Zurmi ta jihar Zamfara. Rahotanni sun bayyana cewar…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe gomman mutane a Filato

‘Yan bindiga sun kashe gomman mutane a Filato

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga jihar Filato sun ce, akalla mutum 145 ne suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren da ‘yan bashin daji suka kai a kan kauyuka 23 a sassan jihar. Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, ‘yan bindigar sun kashe mutum 113 a kauyuka 20 a yankin Karamar Hukumar Bokkos, sannan mutum 32 a wasu kauyuka uku da ke yankin Karamar Hukumar Barkin Ladi a jihar. Bayanai sun ce an kai hare-haren ne cikin daren Asabar zuwa safiyar Litinin da ta gabata, inda aka kashe gomman jama’a tare da jikkata wasu da dama da kuma lalata dimbin dukiya. Ya…
Read More
Ku yi koyi da karantarwar Yesu, kiran Gwamna Sule ga al’ummar Kirista

Ku yi koyi da karantarwar Yesu, kiran Gwamna Sule ga al’ummar Kirista

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiya Abdullahi Sule, ya yi kira ga al’ummar Kirista na Jihar Nasarawa da kewaye da su yi koyi da karantarwar Yesu Kristi, yayin bukukuwan Kirsimeti na wannan shekara. Bayanin haka na kunshe ne cikin sakon Kirsimetin da Gwamna Abdullahi Sule ya mika wa al’ummar jihar a birnin Lafia ta bakin hadiminsa kan sha’anin yada labarai da hulda da jama’a, Dr. Nawani Aboki. Gwamna sule ya ce haihuwar Yesu Krist alama ce mai nuni da a so juna, yafiya, taimakeniya, hakuri da kyautata wa juna da sauransu. Daga nan, ya bukaci al’ummar Kirista da su…
Read More
Tinubu ga ‘yan Nijeriya, ku saurari samun walwala nan ba da daɗewa ba

Tinubu ga ‘yan Nijeriya, ku saurari samun walwala nan ba da daɗewa ba

Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbaci kan su sa ran samun walwala nan ba da dadewa ba. Tabbacin Shugaban na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa kan tsadar rayuwar da suke fuskanta wadda cire tallafin mai ya haifar. Tinubu ya ba da tabbacin haka ne a sakon Kirsimetin da ya aike wa ‘yan kasa, musamman mabiya addinin Kirista, albarkacin bikin Kirsimetin da al’ummar Kirista ke gudanarwa a wannan Litinin a duk fadin duniya. Shuagaban ya ce gwamnatinsa ta bada himma ainun wajen aiwatar da ingantattun matakan da za su…
Read More
Abubuwa 3 masu dakatar da nasarar mai sana’a – Likitan Sana’a

Abubuwa 3 masu dakatar da nasarar mai sana’a – Likitan Sana’a

Daga AMINA YUSUF ALI Ga wasu shawarwari da Badamasi Aliyu Abdullahi ya bayar ga masu sana'a don samun cigaba. Kamar yadda muka sani, kowacce cuta da maganinta. Don haka wasu abubuwa uku da Likitan sana'a ya rawaito cewa idan an guje su za a samu nasara a sana'ar da ake yi. Na farko, jiran tallafin gwamnati wanda ba ka san ranar zuwan sa ba: Masu sana'a da yawa suna tafka wannan kuskuren. Wasu kafin fara sana'arsu. Wasu bayan sun fara. Ga duk mai sana'a, babban strategy ɗin da za ka dauka da zai taimake ka shi ne, kar ka tsara…
Read More
Kawar da ciwon hanta kafin 2030

Kawar da ciwon hanta kafin 2030

A baya-bayan nan ne kasashen duniya suka gudanar da bikin ranar yaki da cutar 'Hepatitis' wanda ake kira da ciwon hanta a Hausance, domin kara wayar da kan jama’a game da wannan mummunar cuta da ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Hepatitis ya kasu iri daban-daban har guda biyar, inda suka hada da; Hepatitis A, da Hepatitis B, da Hepatitis C, da Hepatitis D, da kuma Hepatitis E. Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, kimanin mutum miliyan 325 ke fama da ciwon hanta nau'in B da C a duniya. A yayin da ciwon hanta nau'in B kawai ke kashe…
Read More