Editor

9513 Posts
Sengbe Pieh: Bawan da ya yi wa Turawa tawaye

Sengbe Pieh: Bawan da ya yi wa Turawa tawaye

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A shekara ta 1839, an saci Sengbe Pieh, wani manomi kuma ɗan tireda daga Saliyo a matsayin bawa. Kan hanyar zuwa Amurka ya jagoranci tawaye a cikin jirgin ruwan jigilarsu, abin da ya kawo ƙarshen cinikin bayi a Amurka. Babu dai takamaimen lokacin da ake iya cewa shi ne lokaci da aka haifi Sengbe Pieh, sai dai masana tarihi sun yi ittifakin cewa, an haife shi ne a shekarar 1814 a ƙasar da a yanzu ake kira Saliyo. An yi imanin an haife shi a wani tsibiri da ke gundumar Bonthe, wajen da ya yi ƙaurin…
Read More
Yanzu-yanzu: ‘Yan bindiga sun sace manajan bankin a Zamfara

Yanzu-yanzu: ‘Yan bindiga sun sace manajan bankin a Zamfara

Daga BASHIR ISAH Da tsakar daren Litinin wasu lyan bindiga suka yi dirar mikiya a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara, sannan suka yi awon gaba da manajan Bankin Taj reshen Gusau Malam Mansur A. Kaura a gidansa da ke yankin. MANHAJA ta tattaro cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12 na dare. Majiyarmu ta ce haran sun kai harin ne ɗauke da muggan makamai, kuma sun yi harbe-harben bindiga don razanar da jama'a kafin daga bisani suka tinkari gidan manajan bankin suka yi gaba da shi.
Read More
UTME 2024: JAMB ta saki ƙarin sakamako

UTME 2024: JAMB ta saki ƙarin sakamako

Daga BASHIR ISAH Hukumar shirya jarrabawar neman gurbin karatu a manyan makarantu, JAMB, ta sanar cewar ta saki ƙarin sakamako na jarrabawar UTME na 2024 da ɗalibai suka rubuta kwanan baya. JAMB ta ce ƙarin sakamako 531 da fitar ɓangare ne na sakamako sama da 64,000 da ta riƙe na jarrabawar UTME na bana saboda wasu dalilai. Kawo yanzu, adadin sakamakon da hukumar ta fitar jarrabawar UTME ɗin ya kama 1,842,897. Mai magana da yawun hukumar, Fabian Benjamin, ya faɗa a ranar Talata cewa, hukumar na ci gaba da nazarin batun ɗaliban da ke da matsalar tantancewa kafin daga bisani…
Read More
AEDC, Kaduna DisCo sun zabtare farashin wutar lantarki

AEDC, Kaduna DisCo sun zabtare farashin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Kamfanin raba lantarki na Abuja Electricity Distribution Company (AEDC) ya ba da sanarwar rage farashin wutar lantarkin da yake raba wa kostomominsa na runukunin Band A daga N225/kWh zuwa N206.80/kWh. A ranar Litinin AEDC ya bayyana haka saƙon dabya wallafa a shafinsa na X. Sanarwar ta ce, “Muna farin cikin danar da rage farashin wuta ga kostomominmu na Band A, an yi ragin ne daga N225/kWh zuwa N206.80/kWh wanda ya fara aiki daga yau, 6 ga Mayu, 2024." Kamfanin ya kuma bai wa abokan mu'amalarsa na Band A ɗin tabbacin samun wutar lantarki na sa'o'i 20 zuwa…
Read More
Saƙo zuwa ga iyayen gida

Saƙo zuwa ga iyayen gida

Daga FATIMA GARBA DANBORNO Sakona zuwa ga mata shi ne, su rage dogon buri. Su gane auren mai kuɗi ba shi ba ne ƙarshen auren ba. Idan har suka ce sun dage sai mai kuɗi, ƙarshe sai kin ga an zo ana danasani. Su yi iya yinsu su dage da addu'a babu dare babu rana, akan Allah ya yi masu zaɓi da mafi alkhairi. Sau tari auren wani mai kudin ba alkhairi ba ne. Amma daga lokacin da mace ta kai goshinta ƙasa ta yi addua akan Allah ya yi mata zaɓi da miji na gari mai tsoron Allah, mai…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga a Jihar Kaduna sun kashe mutum shida a wani hari da suka kai ƙauyen Ambe da ke yankin Ƙaramar Hukumar Sanga a jihar a ranar Lahadi da daddare. Mai magana da yawun Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, Mansir Hassan, shi ne ya tabbatar da faruwar hakan, tare da cewa an kama mutum guda da ake zargi da hannu a harin. A cewar Hassan, bayan da 'yan sandan yankin da rudunan Operation Safe Haven, daga suka tinkari mahara inda aka suka yi musayar wuta wanda a ƙarshe aka samu nasarar damƙe guda daga 'yan bindigar sannan…
Read More
Me ake cewa ciwon sanyi na mata?

Me ake cewa ciwon sanyi na mata?

Daga AISHA ASAS Idan aka ce ciwon sanyi, akan samu bambancin fassara daga mutane da dama, wanda ke kawo ruɗani, har matan su kasa bambance wane ne haƙiƙanin ma'ana ta wannan ciwo da ake wa laƙabi da na sanyi. Wasu da dama suna kiran ciwon sanyi a matsayin cuta da ake kamuwa da ita ta hanyar kwanciyar aure, inda suke bayanin ta a matsayin cuta da ake saka wa mata. Wasu kuwa suna fassara ciwon da cutar da ake samu sakamakon rashin tsaftace al'aura, kama daga rashin wanke kamfai akai-akai, rashin amfani da shi, rashin tsaftace wurin da abin da…
Read More
Fashin daji ya zama ‘harkar kasuwanci’ ga wasu jami’an tsaro da na gwamnati — Gwamnan Katsina

Fashin daji ya zama ‘harkar kasuwanci’ ga wasu jami’an tsaro da na gwamnati — Gwamnan Katsina

Daga BASHIR ISAH Gwamman Jihar Katsina, Dikko Radda, ya yi zargin akwai jami'an tsaro da na gwamnati da ke taimaka wa 'yan fashin daji wanda a yanzu hakan ya za zama tamkar ''harkar kasuwanci'' a gare su. Dikko ya bayana haka ne a hirar da tashar Channels Television ta yi da shi a ranar Juma'a. Ya ce, "Yanzu lamarin ya zama sana'a. Harkar kasuwanci ta masu aikata manyan laifuka, wanda ake samun hannun wasu ma'aikatan gwamnati da jami'an tsaro a ciki. "Wannan na daga cikin tarin dalilin dalilan suka sa har yanzu aka kasa ganin bayan ayyukan 'yan fashin daji."…
Read More
IKEDC ya rage farashin wutar lantarki

IKEDC ya rage farashin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Kamfanin Ikeja Electricity Distribution Company ya rage wa kostomominsa na rukunin Band A kuɗin wuta da za su biya zuwa N206.80 kan kowane kilowat a sa'a guda maimakon N225 da hukumar kula da lantarki, NERC a taƙaice ta amince da shi. Mai magana da yawun IKEDC, Olufadeke Omo-Omorodion, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar a ranar Litinin. Sanarwar ta ƙara da cewa, ragin kuɗin wutar zai fara aiki ne daga ranar Litinin, 6 ga Mayu, 2024. Haka nan, ta ce a maimakon N225/Kwh da kostomominsu na Band A su biya bisa la'akari da…
Read More
Ƙarancin ruwa na jikkata majinyata a asibitin Dutse

Ƙarancin ruwa na jikkata majinyata a asibitin Dutse

*Gwamnatin Jigawa ta samar da inji – Shugaban asibitin Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Ƙarancin ruwan sha ya addabi babban asibitin kwanciya na Dutse, Babban Birnin Jihar Jigawa, wato Dutse General Hospital, lamarin da ya sa marasa lafiya da masu zaman jiyya yin gararambar neman ruwan sha a unguwannin Maranjuwa, Fagoji Bakwato da bakin kasuwar ’yan Tifa da ke birnin na Dutse. Kamar yadda binciken Wakilin Blueprint Manhaja ya nuna, ta kai ta kawo marasa lafiya da masu zaman jiyya sun koma yin alwala da ruwan leda da ake kira da ‘pure water’ na Naira 20 ƙwaya ɗaya da…
Read More