08
May
Daga BASHIR ISAH Hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC, za ta gurfanar da 'yar gidan tsohon Minista Hadi Sirika, Fatimah, tare da wasu mutum biyu a kotu a ranar Alhamis. Ana zargin waɗanda lamarin ya shafa ne da laifin badaƙalar kwangila ta sama da Naira biliyan 2.7 a ƙarƙashin Ma'aikatar Aufurin Jirgin Sama ƙarƙashin jagorancin Sirika. Gobe Alhamis shi ne zai zama karon farkon da Sirika zai gurfana a gaban Alƙali Sylvanus Oriji a Babbar Kotun Abuja. Ana sa ran Sirika ya bayyana a gaban kotu tare da wasu mutum uku, ciki har da 'yarsa Fatima da kuma kamfanin Al-Duraq…
