Editor

9513 Posts
Sojoji 36 ‘yan bindiga suka kashe a Neja – Hedikwatar Tsaro

Sojoji 36 ‘yan bindiga suka kashe a Neja – Hedikwatar Tsaro

Daga BASHIR ISAH Hedikwatar Tsaro (DHQ) da ke Abuja ta bayyana cewa, sojoji 36 'yan bindiga suka kashe a Jihar Neja. A ranar Lahadin da ta gaba 'yan bindiga suka yi wa sojoji kwanton-ɓauna a hanyar Zungeru zuwa Tegina inda suka kashe sama da sojoji 20. Sai dai mai magana da yawun babban ofishin tsaro na ƙasa, Manjo Janar Edward Buba, ya ce askarawa 36 ne suka mutu a harin. Buba ya bayyana haka ne a wajen taron manema labarai na mako-mako da ya shirya inda ya yi ƙarin haske game da adadin sojojin da 'yan bindigar suka kashe da…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ɗage shari’ar zargin wawushe N6.9bn kan Emefiele

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ɗage shari’ar zargin wawushe N6.9bn kan Emefiele

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Abuja, ta ɗage ci gaba da sauraron shari'ar sabon zargin da Gwamnatin Tarayya ke yi wa tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, na yin sama-da-faɗi da kuɗin gwamnati Naira biliyan 6.9. A ranar Alhamis aka gurfanar da Emefiele tare da wata Sa’adatu Yaro da kamfaninta mai suna April1616 Investment Limited bisa zargin laifuffuka 20 da suka haɗa da haɗin baki, amfani da haramtattun damammaki da sauransu. Laifukan da aka ce sun saɓa wa Sashe na 19 na Dokar Laifukan Rashawa da Dangoginsu na Dokar 2000. Sai dai zaman shari'ar…
Read More
Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Daga BASHIR ISAH Ya zuwa ranar Litinin ta makon gobe idan Allah Ya kai mu ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa da ya naɗa. Sanarwar da ta fito ta bakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ta ce bikin rantsarwa zai gudana ne a babban zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da misalin ƙarfe 10 na safe. Sanarwar ta ƙara da cewa 'yan rakiya biyu-biyu kacal aka amince wa ministocin su take musu baya zuwa wajen taron. “Ana sa ran ministocin kowanne ya zo da 'yan rikiya guda biyu. “Sannan…
Read More
Ingantaccen rubutu shi ke kai marubuci ko’ina a duniya – Rahmatu Lawan

Ingantaccen rubutu shi ke kai marubuci ko’ina a duniya – Rahmatu Lawan

"Manhajar Hikaya ba ta ɗora littattafan batsa" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Masu bibiyar wannan shafi na Adabi muna yi muku fatan alheri a kodayaushe. Kamar kowanne mako, yau muna ɗauke ne da wata tattaunawa da muka yi da Hajiya Rahmatu Lawan Ɗalha, wata ƙwararriya a harkar sarrafa fasahar sadarwa wacce ita da mijinta masanin fasahar zamani suka samar da Bakandamiya Hikaya, wasu tagwayen manhajoji da ke ba da gudunmawa ga cigaban rubutun adabi da rayuwar marubuta. Ɗaya manhaja ce ta ƙarfafa zumunci tsakanin marubuta da masu karatun littattafansu, sai kuma manhajar tallata littattafai da rubuce-rubuce na ilimi. A tattaunawar da…
Read More
Tinubu ya raba wa ministcoinsa ma’aikatu

Tinubu ya raba wa ministcoinsa ma’aikatu

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanar da ma'aikatun da ministocinsa za su riƙe. A ranar Laraba Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana jerin sunayen sabbin ministocin da kuma ma'aikatar da kowannensu zai jagoranta: Ga jerin sunayen ministcoin da ma'aikatunsu: Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani - Bosun Tijani Ƙaramin Ministan Muhalli - Ishak Salaco Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki - Wale Edun Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki - Bunmi Tunji Ministan Lantarki - Adedayo Adelabu Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al'umma - Tunji Alausa Ministan Ma’adinai - Dele Alake Ministan Yawon Buɗe-Ido - Lola Ade-John Ministan Sufuri - Adegboyega…
Read More
Matsalar tsaro a Arewa: Manoma a yankunan karkara suna ƙara fuskantar matsala a daminar bana

Matsalar tsaro a Arewa: Manoma a yankunan karkara suna ƙara fuskantar matsala a daminar bana

Daga NAFI’U SALISU Al’amarin rashin tsaro a Arewacin Nijeriya, abu ne da ya daɗe yana ci wa al’umma tuwo a ƙwarya, wanda kuma ya haifar da rashin kwanciyar hankali, walwala da shiga halin ni ‘yasu musamman a yankunan karkara da ‘yan bindiga ke cin karensu babu babbaka. Ayyukan ‘yan bindiga da garkuwa da mutane, ya yi sanadin rasa rayukan miliyoyin al’umma, tare da dukiya mai tarin yawa, da kassara ayyukan noma da kiwo a karkara. Hakazalika, ayyukan ‘yan bindigar ya yi sanadin lalacewar dubban garuruwa da a yanzu haka suka zamo kufai babu kowa a cikinsu, yayin da waɗanda suka…
Read More
Hana wani, hana kai: Kanawa me yake damun ƙwaƙwalenmu ne?

Hana wani, hana kai: Kanawa me yake damun ƙwaƙwalenmu ne?

Daga ABDULLAHI JIBRIL LARABI Hassada! ƙyashi! Mugun baki! Sun jawo abinda ya samu 'yar uwarmu Maryam Shetty na alheri sai da aka yi mata sanadin da ta rasa, mu ma kuma muka rasa. Wasu za su ce ita ce dai ta rasa amma mu bamu rasa ba! To Wallahi mu ma mun rasa!. Maryam Shetty Matashiyar ce kamar yadda muke ta ƙarya da Ihun cewar; mun gaji da Mulkin Tsoffin nan da suke gana mana azaba. Yanzu muna son matasa su ma su fito a dama da su. Maryam Shetty ta samu damar da za a dama da ita a…
Read More
Mu tuna da ’yan uwa da maƙwaftanmu

Mu tuna da ’yan uwa da maƙwaftanmu

Tare Da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ya zama dole a daidai wannan lokaci a ƙara yin kira ga jama'a, saboda halin da aka shiga cikin ƙasa, dangane da ƙuncin talauci da tsadar rayuwa da ake cigaba da fuskanta. Kai ka ce rubuce-rubuce da surutai da muke ta yi a baya ta bayan kunnen shugabanni suke bi, ba a sauraron kukanmu da shawarwarinmu, bisa la'akari da yadda abubuwa suke qara taɓarɓarewa, a maimakon a samu sassauci. Lura da yadda abubuwa ke cigaba da lalacewa a cikin ƙasa, sai mutum ya fara tunanin ko ma dai wannan faɗakarwa da ake ta yi ga…
Read More
Shawara game da samun maslaha tsakanin surukai

Shawara game da samun maslaha tsakanin surukai

Tare Da AMINA YUSUF ALI Barkanmu da jimirin karatun jaridarku mai farin jini ta Manhaja. Za mu ci gaba daga inda muka tsaya a kan dalilan da suke kawo lalacewar alaƙa tsakanin surukai. Ta yadda surukuta a ƙasar Hausa ta zama kamar gaba a tsakaninsu. Kowa kishi da hassada yake wa ɗanuwansa. Ga rainin wayo, abin ba a magana. A wani lokaci a baya mun kawo wasu daga cikin dalilan da suka sa hakan take faruwa domin masu karatu su yi alƙalanci su gano wai shin ma laifin wanene? To a yanzu za mu ci gaba da kwararo muku bayani…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe ango da amarya a Filato

‘Yan bindiga sun kashe ango da amarya a Filato

Daga WAKILINMU Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun kashe wasu ma'aurata da suka yi aure ba da daɗewa ba a Jihar Filato. Amarya da angon sun cim ma ajali ne a lokacin da 'yan bindigar suka kai hari a makarantar BECO Comprehensive High School, da ke Kwi cikin Ƙaramar Hukumar Riyom a Jihar Filato. Kazalika, an ce maharan sun ji wa wasu da dama rauni, ciki har da mataimakin shugaban makarantar. Majiyarmu ta ce an kai harin ne a lokacin da malaman makarantar ke tsaka da tattauna yadda za su gudanar da bikin raba kyaututtuka ga ɗaliban makarantar…
Read More