Editor

9513 Posts
Gwamnatin Kano ta fara bincike kan zaftare wa ma’aikata albashi

Gwamnatin Kano ta fara bincike kan zaftare wa ma’aikata albashi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta dakatar da cire Naira 370 na kowane wata daga albashi da fansho na ma’aikatan gwamnatin jihar. Sakataren gwamnatin jihar Abdullahi Baffa Bichi a wata takarda da ya aike wa ɗaukacin shugabannin hukumomin a ranar Litinin wacce Manhaja ta gani a ranar Talata ta ce, an dakatar da cire kuɗaɗen nan take har sai an kammala bincike kan tsarin. Gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ce ta ƙaddamar da wannan tsarin wanda ake zuba kuɗaɗen da aka cire a asusun wani kamfani mai suna Share Benefit Investment Limited. Sakataren ya…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe mutum uku a Kaduna

‘Yan bindiga sun kashe mutum uku a Kaduna

Sun yi garkuwa da wasu da dama Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga Jihar Kaduna sun ce, aƙalla mutum uku sun mutu yayin da aka yi garkuwa da wasu dama sakamakon harin da 'yan bindiga suka kai garin Sabon Layi cikin yankin Ƙaramar Hukumar Birnin-Gwari da ke jihar. Duk da dai ya zuwa haɗa wannan labari babu wani bayani a hukumance kan batun daga ɓangaren hukuma, sai dai wani jigo a yankin da lamarin ya faru, Anas Musa, ya tabbatar da aukuwar harin ga jaridar News Point Nigeria a ranar Juma'a. A cewar Musa, 'yan bindigar sun dira ƙauyen ne da…
Read More
Rigimar Majalisar Dokokin Nasarawa: Mambobin ɓangaren Ogazi na canja sheƙa zuwa ɓangaren Balarabe

Rigimar Majalisar Dokokin Nasarawa: Mambobin ɓangaren Ogazi na canja sheƙa zuwa ɓangaren Balarabe

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Idan ba a manta ba a 'yan kwanakin nan ne Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta tsunduma cikin rikici da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa jim kaɗan bayan zaɓen kujeral Kakakin Majalisar wanda aka so a gudanar a lokacin amma bai yu ba, inda a ƙarshe aka samu ɓangarori 2 tsakanin mambobin majalisar inda wasu ke goyon bayan tsohon kakakin majalisar, Ibrahim Balarabe Abdullahi wanda ke neman zarcewa a kujerar, yayin da wasu kuma ke tare da Ogah Ogazi da shi ma yake neman hawa kujera. Kodayake a lokacin ma fi yawan 'yan majalisar…
Read More
Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata batun yi wa Tinubu da gwamnoni ƙarin albashi

Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata batun yi wa Tinubu da gwamnoni ƙarin albashi

Daga BASHIR ISAH Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu bai amince da wani ƙarin albashi ga zaɓaɓɓun 'yan siyasa da ma'aikatan fannin shari'a ba kamar yadda rahotanni suka nuna. Mai magana da yawun Tinubu, Dele Alake, shi ne ya bayyana hakan cikin sanarwar da ya fitar ranar Alhamis. Alake ya bayyana haka ne a matsayin martani ga rahoton da aka yaɗa kan cewa Shugaban Ƙasar ya amince da ƙarin albashi da kashi 114 wa kansa da mataimakinsa, gwamnoni da ma ma'aikata a ɓangaren shari'a. Tun farko, an ga rahoton da ya ce Hukumar Tarawa da Raba…
Read More
Shari’ar nasarar Tinubu: Lauyoyin Tinubu sun zargi Manhajar Amazon da haifar da matsalar da INEC ta samu da Rumbun IReV

Shari’ar nasarar Tinubu: Lauyoyin Tinubu sun zargi Manhajar Amazon da haifar da matsalar da INEC ta samu da Rumbun IReV

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ta bakin lauyoyinsa, ya shaida wa Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa cewa Rumbun Adana Bayanai a Yanar Gizo na Amazon, ba shi da garanti, ya na iya samun matsala. Sai dai kuma wani ƙwararren injinijya na Amazon ya ƙaryata lauyoyin Tinubu ɗin. AWS Incorporated a ƙarƙashin Amazon ne suka buɗe wa INEC Rumbun Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe ta IReV, a lokacin zaven 2023. Atiku da Peter Obi duk sun ƙalubalaci ƙin watsa sakamakon zaɓe, wanda su ka ce ba a watsa a IReV ba, kamar yadda INEC ta yi alƙawarin…
Read More
Shugabannin Afrika sun miƙa kukansu a taron Paris

Shugabannin Afrika sun miƙa kukansu a taron Paris

Shugabannin ƙasashen Nijar Benin da kuma Ghana sun miƙa kokensu ga taron yanayin da ke gudana a birnin Paris kan yadda manyan ƙasashe ke mayar da hankali wajen zuba maƙuden kuɗi a Ukraine ba tare da duba halin da nahiyar Afrika ke ciki ba, koken da ke zuwa a dai dai lokacin da Amurka ta sanar da shirin zuba ƙarin dala biliyan 1 da miliyan 300 don farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar mai fama da yaqi. Shugabannin ƙasashen na Ghana Benin da kuma jamhuriyyar Nijar yayin jawabinsu gaban taron yanayin wanda ke ci gaba da gudana a birnin Paris na…
Read More
Ina goyon bayan sauye-sauyen da Gwamna Raɗɗa ke yi a Jihar Katsina – Masari

Ina goyon bayan sauye-sauyen da Gwamna Raɗɗa ke yi a Jihar Katsina – Masari

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari ya bayyana ra'ayinsa akan salon kamun ludayin Gwamnan jihar, Malam Dikko Umar Raɗɗa. Masari ya bayyana ra'ayin na sa ne da yake jawabi a wurin wani taron liyafar cin abincin dare da Dattawan Jam'iyyar APC na jihar Katsina suka shirya domin karrama shi tare da yin addu'o'in samun nasara ga sabon Gwamnan da ta gudana a ɗakin taro na Paramount dake cikin birnin Katsina. A cewar Gwamna Masari, yana tare da Dikko Raɗɗa ɗari bisa ɗari kuma yana goyon bayan sauye-sauyen da yake yi domin inganta…
Read More
An yi kira ga sabbin jami’an hana fasa ƙwauri 335 da aka yaye a Kano su zama jakadu nagari

An yi kira ga sabbin jami’an hana fasa ƙwauri 335 da aka yaye a Kano su zama jakadu nagari

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Kwalejin Horas da Jami'an Hana Fasa Ƙwauri ta Ƙasa dake Gordon dutse a jihar Kano ta yaye sabbin jami'ai da suka kammala karvar horo guda 335. Taron wanda ya samu baquncin mataimakin kwanturola na qasa mai kula da sashin bincike, Muhammad Abba Kurra. Da yake jawabi mataimakin kwanturola janar na hukumar ya ce waɗanda aka yaye ɗin su zama jakadun hukumar a duk inda za a kaisu, aikinsu nagari zai ƙarawa hukumar daraja akasin haka kuma zai zubar musu da kima. Ya yi kira gare su akan su yi aiki da doka da ƙa'ida ta…
Read More
Sabbin Hafsoshin Soja: Janar-Janar 103 na fuskantar ritaya

Sabbin Hafsoshin Soja: Janar-Janar 103 na fuskantar ritaya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Baya ga shirin ritayar da ake shirin yi, za a kara wa jami’ai da dama ƙarin girma zuwa matsayi na gaba don cike guraben da manyan hafsoshin da suka yi ritaya za su samar a wani vangare na sake tsara ayyukan da sabbin shugabannin ma’aikata ke yi. Hakan dai na faruwa ne watanni shida bayan da manyan hafsoshin soja 24 da birgediya-janar 38 suka yi ritaya a watan Disambar da ta gabata bayan shafe shekaru 35 suna hidimar ƙasar. Tinubu ya sanar da murabus ɗin Janar Lucky Irabor wanda shi ne babban hafsan tsaron…
Read More