23
Jun
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta bada umarnin mayar da tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara wanda aka tsige, wato Mahadi Aliyu Gusau kan kujerarsa. Mahadi dai shi ne Mataimakin Gwamna zamanin mulkin tsohon Gwamna Bello Matawalle, wanda aka tsige saboda ya ƙi bin shi Jam’iyyar APC daga PDP. Mahadi da PDP ne suka shigar da ƙarar suna ƙalubalantar tsige shi da Majalisar Dokokin Jihar ta yi a watan Fabrairun 2022. Da yake yanke hukunci a ranar Laraba, Alƙalin kotun, Mai Shari’a Inyang ya ce matakin da tsohon Gwamna Matawalle da kwamitin…
