Editor

9513 Posts
CITAD ta gina ‘bukkar Intanet’ ta sama da Naira miliyan 30 a Jama’are

CITAD ta gina ‘bukkar Intanet’ ta sama da Naira miliyan 30 a Jama’are

Daga IBRAHIM HAMISU a Bauchi Cibiyar Bunƙasa Fasahar Sadarwa da Cigaban Al'umma CITAD ta samar da wata 'bukkar Intanet", kana ta damƙawa al'ummar garin Jama'are da ke Jihar Bauchi, aka kuma ƙaddamar da ginin bukkar a hedkwatar Ƙaramar Hukumar Jama'are ranar Asabar da ta gabata. Babban Daraktan Cibiyar Bunƙasa Fasahar Sadarwa da Cigaban Al'umma CITAD Engr. Yunusa Zakari Ya'u ya bayyana cewa a cikin wannan tsari mai taken Digital Hub za su gina ire-iren wannan bukka ta intanet guda 20 cikin shekara ɗaya a faɗin Nijeriya. Y. Z. ya ce: "Kwamfutocin da ke cikin wannan bukka ba kamar sauran kwamfutoci…
Read More
Ramadan: Gwamnatin Katsina za ta ciyar da mutum 72,000 abincin buɗa-baki

Ramadan: Gwamnatin Katsina za ta ciyar da mutum 72,000 abincin buɗa-baki

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Dikko Umar Raɗɗa ta bayyana cewar za ta ciyar da al'umar jihar dafaffen abinci don yin buɗa-baki tun daga farko zuwa ƙarshensa azumin Ramadan na bana. A cewar sanarwar da gwamnatin jihar ta fitar, za riƙa ciyar da al'umar jihar dubu 72,000 a kowace rana a cibiyoyi daban-daban da za a buɗe a faɗin jihar. Hakan na nufin za a ciyar da mutane milyan 2,000,000 cikin watan mai alfarma na shekarar 1445 AH/2024. Kazalika, Gwamnan Jihar ya ba da umurnin fara sayar da masara, gero da kuma dawa na gwamnati…
Read More
Ku nemi watan Ramadan daga ranar Lahadi — Sarkin Musulmi

Ku nemi watan Ramadan daga ranar Lahadi — Sarkin Musulmi

Daga BASHIR ISAH Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Musulunci a Nijeriya (NSCIA), Sa’ad Abubakar, ya buƙaci al'ummar Musulmi da a nemi jinjirin watan Ramadan na shekarar 1445AH daga ranar Lahadi, 10 ga Maris, 2024. Umarnin hakan na ƙunshe ne a sanarwar da ke ɗauke da sa hannun Farfesa Sambo Janaidu wanda ya kasance Shugaban Kwamitin Shawara na Majalisar Masarautar Sakkwato wadda aka raba wa manema labarai a ranar Asabar. Sanarwar ta ce: “Ana sanar da Al'ummar Muslim kan cewa su fara neman jinjirin watan Ramadan daga ranar Lahadi, 10 ga Maris wanda ya yi daidai da 29…
Read More
An rantsar da kantomomin riƙon ƙananan hukumomi a Kebbi

An rantsar da kantomomin riƙon ƙananan hukumomi a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Ranar Talatar da ta gabata ne a Jihar Kebbi aka rantsar da ƙarin kwamishina ɗaya da shugabannin riƙo na ƙananan hukumomi 21 da ke akwai bayan rushe majalisun ƙananan hukumomin a cikin watan da ya gabata. Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala rantsar da shugabannin, Gwamna Nasir Idris ya yi kira ga al'ummar jihar Kebbi da su ci gaba da bai wa wannan gwamantin goyon baya don ganin ta aiwatar da ayyukan ci gaba da ta yi alƙawari a baya lokacin yaƙin neman zaɓe. "Wannan gwamnatin ta kowa da kowa ce da matasa…
Read More
Kuriga: Shettima ya gana da iyayen ɗaliban da aka yi garkuwa da su

Kuriga: Shettima ya gana da iyayen ɗaliban da aka yi garkuwa da su

*Ya ba da tabbacin ceto yaran cikin ƙoshin lafiya Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya gana da shugabannin ƙauyen Kuriga, Jihar Kaduna da kuma iyayen ɗaliban firamaren da ɓarayin daji suka yi garkuwa da su kwanan nan a yankin. Kusan ɗalibai 300 daga makarantar firamare da GSS da ke Kuriga cikin Ƙaramar Hukumar Chikun a jihar, 'yan bindiga suna yi awon gaba da su a farkon makon jiya. Sai dai a tattaunawar da suka yi a Fadar Gwamnatin Jihar a ranar Asabar, Shettima ya bada tabbacin gwamnati ta yanke shawarar ceto ɗaliban da lamarin ya shafa baki…
Read More
Lawal ya ƙaddamar da ofishin Asusun Inganta Tsaron Zamfara

Lawal ya ƙaddamar da ofishin Asusun Inganta Tsaron Zamfara

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta tallafa wa Asusun Inganta Tsaron Jihar ɗari bisa ɗari. Ya bayyana haka ne a ranar Juma'a a lokacin da yake ƙaddamar da ofishin asusun a Gusau, babban birnin Jihar. Mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya ce Kwamitin Asusun Tsaron Zamfara na guda ne ƙarƙashin jagorancin tsohon IGP, MD Abubakar. Idris ya ƙara da cewa, igantaccen aikin da aka yi wajen samar da ginin ofishin ya nuna himmar da Kwamitin Amintattu na asusun ke da shi wajen sauke nauyin da ya rataya a…
Read More
Muna jiran umarni na ƙarshe don buɗe iyakar Nijeriya da Nijar bayan ɗage takunkumin ECOWAS – Kwastom

Muna jiran umarni na ƙarshe don buɗe iyakar Nijeriya da Nijar bayan ɗage takunkumin ECOWAS – Kwastom

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Kwastom ta ziyarci tashar iyakar Nijeriya da jamhuriyar Nijar bayan ɗage takunkumin da ƙungiyar ECOWAS ta ƙaƙaba wa Nijar. Hukumar ta ce ɗage takunkumin da kuma maido da wutar lantarki shi ne dalilan ziyarar tare shirya komai na sake buɗe iyakar Illela. Kazalika ta buƙaci mazauna yankin da masu ruwa da tsaki na al’ummar yankin kan iyakar Illela da ke Sakkwato da su bi ƙa’idojin da aka shimfiɗa gabanin sake buɗe iyakar da jamhuriyar Nijar. Kamal Muhammad, Kwanturolan NCS mai kula da yankin Sakkwato/Zamfara, a ranar Talata, ya ziyarci iyakar Illela. Muhammad ya…
Read More
Gwamnatin Tarayya za ta yaƙi miyagun ɗabi’u tsakanin ɗaliban sakandare

Gwamnatin Tarayya za ta yaƙi miyagun ɗabi’u tsakanin ɗaliban sakandare

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Gwamnatin Tarayya ta yi kira akan haɗin kai wajen yaƙi da miyagun ɗabi'u a makarantun sakandare a faɗin Nijeriya. Maigirma Ministan Ilmi na Ƙasa Honarabul Yusuf Tanko Sununu ne ya yi wannan kiran yayin wata ganawa da wani sashen malamai, ɗalibai da iyayen yara a lokacin wata faɗakarwa akan hanyoyin da za a bi wajen magance matsalolin miyagun ɗabi'u a makarantun sakandare a faɗin Nijeriya. Ministan ya bayyana cewa waɗansu daga cikin hanyoyin da za su magance matsalolin miyagun ɗabi'u tsakanin yara ɗaliban sakandare sun haɗa da sake farfaɗo da ƙungiyoyin makarantun sakandare irin…
Read More
Canjin Dala kashi biyar ne a Nijeriya – Bashir Na’iya

Canjin Dala kashi biyar ne a Nijeriya – Bashir Na’iya

Daga AMINA YUSUF ALI Duk da cewa 'yan kasuwa su ma suna da rawar da za su taka wajen samun sauƙin tsadar kaya, amma ka da mu yi ta jibga musu laifi ba tare da mun dubi yadda canjin dalar kanta ya koma ba a Nijeriya. A halin da ake ciki yanzu a Nijeriya canjin dollar ya kasu kusan kashi biyar, kowa yana da farashinsa na canji. Misali: Canjin CBN daban,Canjin bayan fage ko kamfanonin canji daban,Canjin hukumar kwastam daban,Canjin 'yan Fesbuk ma daban,Canjin mazauna ƙasashen waje daban. Wallahi ni wannan bambanci har dariya yake ba ni, na rasa sanin…
Read More
El-mustapha ya nuna alhini kan rasuwar mahaifiyar Afakallah

El-mustapha ya nuna alhini kan rasuwar mahaifiyar Afakallah

Daga BASHIR ISAH Sakataren Hukumar Tace Finafinai na Jihar Kano, Alh. Abba El-mustapha, ya nuna alhininsa kan rasuwar mahaifiyar tsohon sakataren hukumar, Malam Na'abba Afakallah. Sanarwar da hukumar ta fitar ranar Juma'a ta bakin Jami'in Yaɗa Labarai, Abdullahi Sani Sulaiman, ta ce Hajiya Gwaggo ta rasu ne bayan fama da rashin lafiya. Abba El-mustapha ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa tagari, kuma abar koyi wadda rasuwarta ta haifar da wagegen giɓi a cikin al'umma. Ya ƙara da cewa, mutuwarta babban rashi ne ba ga ahalinta kaɗai ba har ma da al'ummar Musulmi baki ɗaya. Daga nan, El-Mustapha ya yi addu'ar…
Read More