Editor

9513 Posts
La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

Daga MAHDI M. MUHAMMAD La Liga na nazarin wani bidiyo da ake zargin yana nuna wariyar launin fata ga Vinicius Jr a wasan da Real Madrid ta buga da Valencia a ƙarshen makon da ya gabata. Bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta na Intanet ya nuna yadda wani yaro mai goyon bayan Valencia ke jagorantar cin zarafin ɗan wasan. Vinicius ya zura ƙwallaye biyu a wasan da suka tashi 2-2 a ranar Asabar kuma ya yi murna ta hanyar ɗaga hannunsa sama. Ɗan wasan mai shekaru 23 ya fuskanci cin zarafi na wariyar launin fata sau da dama…
Read More
Naira 100,000 ba zai riƙe rayuwar ma’aikaci ba – Majalisar Wakilai

Naira 100,000 ba zai riƙe rayuwar ma’aikaci ba – Majalisar Wakilai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ya zama wajibi a daidaita albashin ma'aikatan Nijeriya, domin kuwa ƙasa da Naira 100,000 a wata ba zai riƙe rayuwar ma'aikaci ba. Majalisar ta ce ɗauki matakin tabbatar da ƙarin albashi ga ma’aikatan Nijeriya. An cimma wannan matsaya ne a zaman da aka yi a ranar Laraba, biyo bayan ƙudirin da shugaban marasa rinjaye Kingsley Chinda da wasu 39 suka gabatar. Yayin muhawara kan ƙudirin mai taken "Buƙatar ƙarin albashin ma'aikata a Nijeriya," mataimakin shugaban marasa rinjaye Aliyu Madaki ya bayyana ƙalubalen da 'yan Nijeriya ke fuskanta sakamakon hauhawar farashin kayayyaki.…
Read More
Hukumar Kwastom za ta binciki sanadin turmutsitsi a wurin cinikin shinkafa

Hukumar Kwastom za ta binciki sanadin turmutsitsi a wurin cinikin shinkafa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Hana Fasa-ƙwauri ta Nijeriya, NCS, ta kafa kwamitin da zai binciki al’amuran da suka janyo turmutsitsin da kuma asarar rayuka da aka samu a tsohon ofishinta da ke Yaba, Legas. Shugaban hukumar Bashir Adeniyi, ya umurci kwamitin ƙarƙashin jagorancin wani jami’in hukumar da ya zaƙulo waɗanda rikicin ya rutsa da su tare da tsara hanyoyin bada tallafi ga iyalansu. Haka zalika, shugaban ya dakatar da rabon ne domin jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu yayin da hukumar da ƙoƙarin samar da dabarun yadda za a cigaba da rabon cikin kwanciyar hankali. Bugu da ƙari, jami’in…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da gomman ɗaliban tsangaya a Sakkwato

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da gomman ɗaliban tsangaya a Sakkwato

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga jihar Sakkwato sun ce, 'yan bindiga sun sace gomman ɗalibai a wata makarantar tsangaya da ke yankin Gidan Bakuso a ƙaramar hukumar Gada da ke jihar. Majiyarmu ta ce an yi awon gaba da ɗaliban ne da misalin ƙarfe 1:00 na dare. Mai makarantar, Malam Liman Abubakar, ya shaida wa majiyar tamu cewa, ba a ga wasu ɗailibai su 15 ba, kuma ana ci gaba da ƙirga ɗaliban da suka ɓata. Abubakar ya ƙara da cewa, yayin harin 'yan bindigar sun harbi mutum guda da bindiga sannan sun ɗauki wata mata. Ya ce “A lokacin…
Read More
Ina farin ciki da matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka – Buhari

Ina farin ciki da matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka – Buhari

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana farin ciki da irin salon mulkin gwamnati shugaba Tinubu duk da halin matsin rayuwa da taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya. Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya kai masa ziyarci a Daura, Jihar Katsina. Shettima ya ce, Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Tinubu ba za ta bar wani abu da zai kawo cikas a yunƙurinta na kare rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya ba. Mataimakin shugaban Nijeriya ta cigaba da cewa, ya sha alwashin cewa gwamnati mai ci za…
Read More
Tsaro: Shugaban Jami’ar Bayero ya buƙaci a samar da kuɗin katange jami’ar

Tsaro: Shugaban Jami’ar Bayero ya buƙaci a samar da kuɗin katange jami’ar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Jami’ar Bayero da ke Jihar Kano, Farfesa Sagir Abbas, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta saki kuɗaɗen da aka ware domin katange jami'ar saboda matsalolin tsaro da ake fama da su. Farfesa Abbas ya bayyana halan ne yayin taron taro karo na 38 da aka gudanar a Jami’ar Bayero a Kano. Abbas ya jaddada muhimmancin waɗannan kuɗaɗe, inda ya bayyana cewa, duk da cewa akwai kaso na farko a cikin kasafin kuɗin tarayya na shekarar 2023, daga baya kuma an cire shi a shekarar 2024, wanda hakan ya sa jami’ar ta shiga cikin mawuyacin hali.…
Read More
Ku dawo da kuɗin tallafi Korona – Majalisar Wakilai ga kamfanonin jiragen sama

Ku dawo da kuɗin tallafi Korona – Majalisar Wakilai ga kamfanonin jiragen sama

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kwamitin Kula da Harkokin Gwamnati na Majalisar Wakilai ya bayar da wa'adin mako guda ga dukkan kamfanonin jiragen sama masu zaman kansu a ƙasar nan da su yi lissafin yadda suka kashe zunzurutun kuɗi har Naira Biliyan 4 da Gwamnatin Tarayya ta ba su don magance cutar COVID-19 ko kuma su dawo da kuɗaɗen. Kwamitin wanda ɗan jam’iyyar PDP daga jihar Osun, Bamidele Salam ya jagoranta, ya bayar da wa’adin ne a ranar Juma’a a wajen ci gaba da zaman bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen shiga a tsakanin ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya. An ruwaito…
Read More
Emefiele: An kwaikwayi Buhari a cire Dala miliyan 6.2 – Ƙwararre a kotu

Emefiele: An kwaikwayi Buhari a cire Dala miliyan 6.2 – Ƙwararre a kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wani ƙwararren ma’aikacin da ya yi nazarin takardun binciken da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa, EFCC, Bamaiyi Haruna, a ranar Alhamis, ya ce, binciken da aka yi kan takardun da aka yi amfani da su wajen fitar da zunzurutun kuɗi har Dala Miliyan 6.2 daga Babban Bankin Nijeriya (CBN) a watan Fabrairun 2023 ya nuna cewa jabu ne sa hannun tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari akansu. Hukumar EFCC ta yi zargin cewa a ranar 8 ga Fabrairu, 2023, tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya haɗa baki da wani…
Read More
An daina sauya wajen hidimar ƙasa – Shugaban NYSC

An daina sauya wajen hidimar ƙasa – Shugaban NYSC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Masu Yi Wa Ƙasa Hidima, NYSC, Birgediya Janar Yusha’u Ahmed, ya ja hankalin masu hidima da su rungumi wuraren da ake tura su tare da bayar da tasu gudunmawar wajen cigaban jihohin da aka ba su. Da yake zantawa da masu hidima na Batch A Stream 1 a yayin bikin shiga sansanin wayar da kai na jihar Anambra, Ahmed ya jaddada muhimmancin mutunta tsarin hidimta wa ƙasa tare da ba da fifiko ga tsaron su. Ya ba da shawarar cewa, “Ku kasance cikin kwanciyar hankali da juriya yayin da ku ke ƙara kima ga yankunan…
Read More
‘Yan daba sun yi wa filin jirgin saman Haiti dirar mikiya

‘Yan daba sun yi wa filin jirgin saman Haiti dirar mikiya

Kwana guda bayan da gungun ‘yan daba suka ɓalle manyan gidajen yari biyu a Haiti, a yau kuma sun farwa babban filin jirgin saman ƙasar da nufin karve iko da shi. Wannan ta sa dole ƙasashen da ke maƙwaftaka da Haiti suka fara ƙarfafa tsaron kan iyakokin su don gudun fantsamar ‘yan dabar zuwa cikin su. Faya-fayan bidiyo sun nuna yadda aka riƙa musayar wuta tsakanin jami’an sojoji da kuma ‘yan dabar sama da 500. Har kawo yanzu filin jirgin saman na The Toussaint Louverture na kulle yayin da aka dakatar da duk wata zirga-zirga. Ko a makon da ya…
Read More