08
Mar
Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya lashi takobin hukunta waɗanda suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada a jihar. Wasu da ake zargin 'yan banga ne suka kashe malamin a makon jiya a garin Mada, cikin Ƙaramar Hukumar Gusau, Jihar Zamfara. Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar ran Juma'a cewa, Gwamna Lawal ya ziyarci garin Mada don yi musu ta'aziyya kan rasuwar malamin, inda a nan ya yi sallar Juma'a a babban masallacin garin. Ya ce, yayin da yake yi wa jama'a jawabi, Gwamna Lawal ya yi alƙawarin zai yi…
