07
Mar
Daga BASHIR ISAH ‘Yan bindiga sun kashe makiyayi ɗaya da dabbobi guda 50 da suka haɗa da shanu da tumaki a wani hari da suka kai ranar Talata a yankin Fanzo da ke ƙaramar hukumar Barkin Ladi a Jihar Fialato. Alhaji Dan-Azumi, wanda ya rasa shanu 21 a harin, ya faɗa wa Daily Trust cewar, maharan sun ji wa wani makiyayi da ke kiwo a yankin rauni. Ya bayyana cewa, “Maharan sun faɗo yankin inda suka yi harbi da bindiga. Sun kashe makiya ɗaya sannan sun jikkata mutum ɗaya. “’Yan bindigar sun yi awon gaba da shanu aƙalla guda 50,…
