21
Feb
Ma'aikata sun tsunduma yajin aiki a Neja Daga BASHIR ISAH Ma'aikatan gwamnati a Jihar Neja, sun fara yajin aikin sai-baba-ta-gani domin biyar haƙƙinsu a wajen gwamnati. Da safiyar Laraba ma'aikatan suka fara yajin aikin bisa umarnin Ƙungiyar Ƙwadago (NLC) reahen jihar, lamarin da ya haifar da tsaiko a harkokin jihar. NLC reshen jihar ta ɗauki wannan mataki ne bayan da gwamnatin jihar ta kasa cimma buƙatun mambobinta a jihar. Shugaban NLC na jihar, Idrees Lafene da takwaransa na ƙungiyar 'yan kasuwa, Ibrahim Gana, su ne suka bai wa ma'aikatan jihar unarnin shiga yakin aikin bisa abin da suka kira gazawa…
