Editor

9513 Posts
MOPPAN ta taya Afakallah murna kan sabon naɗin da aka yi masa

MOPPAN ta taya Afakallah murna kan sabon naɗin da aka yi masa

Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), ƙarƙashin jagorancin Alhaji Habibu Barde, ta miƙa saƙon taya murna da fatan alheri ga Alhaji Ismail Mohammed Na'Abba da aka fi sani da Afakallah. MOPPAN ta taya Afakallah murna ne bisa naɗin da aka yi masa na zama ɗaya daga cikin mambobin Hukumar Gudanarwa na Jami’ar Fasaha ta Jihar Jigawa. Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 19/5/2024 da kuma sa hannun sakatarenta na ƙassa, Al-Amin Ciroma. Ƙungiyar ta ce Afakallah na ɗaya daga cikin zaƙaƙuran mutanen da suka bunƙasa masa’antar shirya finafinan Hausa…
Read More
Yanzu-yanzu: Shugaban Ƙasar Iran ya rasu yana da shekara 63

Yanzu-yanzu: Shugaban Ƙasar Iran ya rasu yana da shekara 63

Rahotanni daga ƙasar Iran sun tabbatar da mutuwar Shugaba Ebrahim Raisi na ƙasar sakamakon hatsarin jirgin sama mai saukar ungulu. An ce jirgin saman ya yi hatsari ne sakamkon rashin kyawun yanayi. Marigayin ya bar duniya yana da shekara 63. Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce an ga buraguzan jirgin a cikin wasu tsaunuka masu sarƙaƙiya. Shugaban ƙungiyar agaji ta Red Crescent a Iran, ya ce masu aikin ceto sun isa wurin da suka ga ɓuraguzan jirgin sai dai babu alamar akwai waɗanda suka tsira. Bayanai sun ce jirgin na ɗauke ne da Shugaba Ibrahim Raisi da ministan harkokin wajensa,…
Read More
Majalisa ta amince wa Tinubu ciyo bashin dala miliyan 500 don sayen mitocin lantarki

Majalisa ta amince wa Tinubu ciyo bashin dala miliyan 500 don sayen mitocin lantarki

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin wutar lantarki ga ’yan Nijeriya. A zaman majalisar na ranar Labara ne ta amince wa Shugaba Bola Tinubu ya karɓo bashin daga Bankin Duniya. Bayan karɓar rahoton kwamitin basukan kasashen waje ne majalisar ta amince da karɓo bashin wanda za a damƙa ga Hukumar Kula da Kamfanonin Gwamnati (BPE). Bashin Dala miliyan 500 da za a sayi mitocin lantarkin da su wani ɓangare ne na bashin Bankin Duniya na Dala biliyan 7.94 da Tinubu ya…
Read More
Gwamna Soludo ya sauke shugabannin ƙananan hukumomi

Gwamna Soludo ya sauke shugabannin ƙananan hukumomi

Gwamnan Jihar Anambra, Chukwuma Soludo, ya sauke shugabannin ƙananan hukumomi 21 da jihar ke da su. Haka nan, Gwamnan ya buƙaci saukakkun ciyamomin da su miƙa ragamar aiki ga shugabannin sassan gudanarwa na ƙananan hukumomin. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwa mai ɗauke da da hannun Kwamishinan Kula da Harkokin Ƙananan Hukumomi da Sarautun Gargajiya na Jihar, Collins Nwabunwanne, da kwanan wata 17 ga Mayu. Ya zuwa ranar Litinin, 20 ga Mayu ake sa ran waɗanda lamarin ya shafa su miƙa ragamar aiki ga waɗanda suka dace. A cewar wasiƙar: “Biyo bayan ƙarewar wa'adinka a matsayin shugaban kwamitin miƙa…
Read More
Yadda Farfesa Wakawa ya bunƙasa asibitin masu lalurar taɓin hankali a Maiduguri

Yadda Farfesa Wakawa ya bunƙasa asibitin masu lalurar taɓin hankali a Maiduguri

Daga GAMBO ISA  Babban Daraktan Likitoci na Jihar Borno, Farfesa Ibrahim Abdullahi Wakawa ya ɗaga likafar Asibitin Masu Fama da Tavin Hankali ta Maiduguri a Babban Birnin Jihar Borno. An bayyana cewa Farfesa Wakawa ya gudanar da manyan ayyuka da dama a wannan cibiyar a matsayin wani ɓangare na gudummawar da ya bayar ga fannin kiwon lafiyar a Nijeriya. Farfesa Wakawa a lokacinsa ya yi ayyuka da yawa a asibitin da suka kasance abin kwatance ga al'ummar Borno, da suka haɗa da, gina wajen gwaje-gwaje na zamani wato Electro-Diagnostic Complex da gyare-gyaren ɗakunan magani, Sashe na 1 na kwamfuta, kayan…
Read More
Hajjin 2024: Tinubu ya tallafa wa maniyyata da Biliyan N90

Hajjin 2024: Tinubu ya tallafa wa maniyyata da Biliyan N90

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta tallafa wa maniyyatan aikin hajjin 2024 da Naira Biliyan 90. Shettima ya bayyana haka ne ranar Laraba a wajen ƙaddamar da fara tashin maniyyatan aikin Hajji na ƙasa na shekarar 2024, wanda aka gudanar a filin jirgin saman Sir Ahmadu Bello International Airport da ke Birnin Kebbi. “Za ku iya tuna cewa, a bana mun fuskanci babban ƙalubale wajen bayyana gundarin adadin kuɗin aikin hajjin 2024, sakamakon yadda farashin canjin kuɗin qasashen waje ya tashi. “Don haka Shugaba Bola Tinubu ya yi aiki…
Read More
Bellingham ya ci wa Real Madrid ƙwallo ta 19

Bellingham ya ci wa Real Madrid ƙwallo ta 19

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jude Bellingham ya ci ƙwallonsa na 19 a wasan da Real Madrid ta lallasa Deportivo Alsves da ci 5 da nema a filin wasa na Santiago Bernabeu. Ɗan wasan Ingila ɗin ne ya fara cin ƙwallo a wasan, wanda shine na farko tun da Real Madrid ta lashe kofin gasar La Liga ta Sifaniya. Ƙwallon da Bellingham ya ci dai ta sa yanzu ya bai wa ɗan wasan gaba na Girona Artem Dovbyk tazarar maki guda a tseren da suke na lashe takalmin zinari, na wanda ya fi saka kowallo a raga. Vinicius Jr ne ya…
Read More
Wajibi ne matasa ku zama masu ƙwazo a Nijeriya – Barista Junaidu

Wajibi ne matasa ku zama masu ƙwazo a Nijeriya – Barista Junaidu

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kabo An shawarci matasa maza da mata na Jihar Kano dama Nijariya bakiɗaya da su tashi tsaye wajen zama masu ƙwazo wajan neman halas domin kuwa ta haka ne matasa shugabannin gobe za su bada kyakkyawan musali ga sauran al'umma a wannan lokaci. Wannan shawara ta fito ne daga baki shugaban gamayyar ƙungiyoyin ’yan kasuwa ta Singa da ake kira Singa Market Development Association Of Nigeria (SMDAN) Barista Junaidu Zakari, a lokacin da ya ke wajabi wajan walimar ɗaurin aure ’ya ga ɗaya daga cikin futattun ’yan kasuwar kano Alhaji Sani Asia, wanda aka gabatar a…
Read More
Ficewar Nijar, Mali da Burkina Faso barazana ce ga tsaro — ECOWAS

Ficewar Nijar, Mali da Burkina Faso barazana ce ga tsaro — ECOWAS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) ta bayyana yunƙurin ficewar ƙasashen Nijar da Chadi da Burkina Faso daga cikinta a matsayin mummunan barazana ga harkokin tsaron yankin. Kwamishinan harkokin siyasa, zaman lafiya da tsaro na ECOWAS, Abdel-Fatau Musah ne ya bayyana hakan a yayin wani zama mai taken: “Daƙile Matsaloli Ta Hanyar Haɗin Gwiwar  Masu Ruwa da Tsaki a Fannin Tsaro A Yankin da Abin Ya Shafa” wanda Ƙungiyar Tarayyar Turai tare da haɗin gwiwar Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci (NCTC) suka shirya a Abuja ranar Laraba. A watan Janairu ne dai ƙasashen uku…
Read More
Jiragen Fadar Shugaban Ƙasa: Za a gurfanar da Nuhu Ribadu gaban majalisa

Jiragen Fadar Shugaban Ƙasa: Za a gurfanar da Nuhu Ribadu gaban majalisa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dokokin Nijeriya za ta gayyaci mashawarcin shugaban ƙasa kan al’amuran tsaro Malam Nuhu Ribadu, saboda lalacewar jiragen Fadar Shugaban Ƙasa. Shugaban kwamitin lura da jiragen fadar shugaban a Majalisar, Satomi Ahmed,  ne ya sanar da hakan. Alhakin kula da jirgin shugaban ƙasa da mataimakinsa dai ya rataya ne a wuyan mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan al’amuran tsaro. Honabul Satomi Ahmed ya ce a kwai kasafin na musamman domin kula da jiragen fadar shugaban ƙasa. Ya ce waɗannan maƙudan kuɗaɗe suna ƙarƙashin ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro…
Read More