Editor

9513 Posts
Gwamnonin Arewa maso-Yamma sun nemi goyon bayan MƊD kan magance ƙalubalen yankin

Gwamnonin Arewa maso-Yamma sun nemi goyon bayan MƊD kan magance ƙalubalen yankin

Daga WAKILINMU Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma na Nijeriya sun yi taro tare da tawagar Majalisar Ɗinkin Duniya, ƙarƙashin jagorancin mai kula da harkokin jinƙai, Mohamed Malick Fall, a Abuja ranar Juma'a. Manufar taron dai ita ce neman tallafi don tunkarar babban ƙalubalen ci gaban yankin. Taron wanda Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma kuma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya jagoranta, ya samu halartar gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani, Injiniya Abba Kabir Yusuf na Kano, Mallam Umar Namadi na Jigawa; Mataimakin Gwamnan Sokoto, Alhaji Idris Muhammad Gobir, da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal. Taron wanda aka…
Read More
Baƙuwar cuta ta kashe mutane 13 a Zamfara

Baƙuwar cuta ta kashe mutane 13 a Zamfara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Adadin mutanen da suka rasu sakamakon kamuwa da wata baƙuwar cuta ya ƙaru zuwa 13 a Jihar Zamfara. Aqalla mutane 505, akasarinsu mata da ƙananan tara ne aka kai asibiti sakamakon kamuwa da cutar a ƙananan hukumomin Gusau, Maradun da kuma Shinkafi a jihar. Haka zalika an samu ɓullar cutar a Jihar Sakkawato a ƙananan hukumomin Isa da Zurmi. A watan Fabrairu aka fara samun ɓullar baƙuwar cutar a ƙauyen Tsibiri da ke Ƙaramar Hukumar Maradun. Wani mazaunin Tsibiri ya ce daga lokacin “Zuwa ranar Lahadi 12 ga Mayu, 2024, mutane 228 ne suka…
Read More
Tinubu ya haramta sayen motoci masu amfani da fetur a ma’aikatun gwamnati

Tinubu ya haramta sayen motoci masu amfani da fetur a ma’aikatun gwamnati

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Tinubu ya haramta sayen motoci masu amfani da man fetur a hukumomi da ma’aikatun gwamnatin Nijeriya. Shugaban ƙasar ya kuma umarci motocin su koma amfani da ababen hawa masu amfani da iskar gas. A jawabinsa ga Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, Shugaba Tinubu, ya ce babu gudu babu ja da baya kan batun komawa amfani da ababen hawa masu amfani da iskar gas a Nijeriya. A cewarsa, hakan na daga cikin matakan da gwamnatinsa ta ɗauka na tabbatar da wadataccen makamashi da kuma rage tsadarsa a ƙasar. Ya kuma ba da umarnin soke duk…
Read More
APC ta dakatar da Hon Aminu Sani Jaji kan yi wa jam’iyya zagon ƙasa

APC ta dakatar da Hon Aminu Sani Jaji kan yi wa jam’iyya zagon ƙasa

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Kwamitin zartarwa na jam'iyyar APC a mazaɓar Birnin Magaji dake ƙaramar hukumar Birnin Magaji, jihar Zamfara, ta dakatar da Hon. Aminu Sani Jaji daga jam'iyyar a kan yi wa jam'iyyar zagon ƙasa yayin zaɓen 2023 a jihar. Aminu Sani Jaji shi ne ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Birnin Magaji da Ƙaura Namoda na tarayya. Dakatarwa na ƙunshe ne a wata wasiƙa da aka gabatar ga shugaban jam’iyyar APC na jiha mai ɗauke da sa hannun shugaban jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin Magaji, Alh. Bello Lawali Maizogale da Salmanu Umar Tsamiya, inda ake zargin Hon.…
Read More
Al-Nakba: Falastinawa ba za su taɓa miƙa wuya ga Isra’ila ba – Ambasada Abu Shawesh

Al-Nakba: Falastinawa ba za su taɓa miƙa wuya ga Isra’ila ba – Ambasada Abu Shawesh

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A rana ta 223 na yaƙin kisan ƙare dangi a akan al'ummar Falastinu, Jakadan Falastinu a Nijeriya Abdullah Abu Shawesh ya bayyana cewa, a cikin shekaru 76 da fara gallaza wa al'ummar Falastinu, ba mu manta ba, ba za mu yafe ba. Al'ummar Falastinawa za su ci gaba da tunkarar mamayar da Isra'ila ke yi, ba za su taba miƙa wuya ba. A wata sanarwa da ya fitar a ranar 16 ga Mayu, 2024, ya ce; "A ranar 15 ga watan Mayu al'ummar Falastinu a duk duniya sun gudanar da bukukuwan cika shekaru 76 na 'Al-Nakba'…
Read More
Juventus ta lashe kofin Italiya bayan shekara uku

Juventus ta lashe kofin Italiya bayan shekara uku

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Juventus ta lashe kofin Italiya karo na 15, bayan da ta doke Atalanta da ci 1-0 a birnin Rome, a wasan da suka fafata ranar Laraba. Ƙwallon ɗaya tilo da Dusan Vlahovic ya zura a mintina na huɗu da fara wasa ya tabbatar da nasarar Juventus, wanda ta lashe Kofin bayan shafe shekaru uku babu labari. Tawagar Massimiliano Allegri da suka kawo matakin ƙarshe da nasara a wasanni uku kacal, sun nuna turjiya, tare da daƙile yunqurin Atalanta na lashe gasar. Ɗan wasan gaban na Serbia ya sake cin wata amma aka soke ta saboda satar…
Read More
Majalisar Dattawa ta amince da kafa Hukumar Raya Arewa maso Yamma

Majalisar Dattawa ta amince da kafa Hukumar Raya Arewa maso Yamma

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Alhamis ne Majalisar Dattijai ta amince da ƙudirin dokar Hukumar Raya Yankin Arewa maso Yamma domin magance ƙalubalen da jihohi bakwai ke fuskanta a yankin. Wannan ya biyo bayan la'akari da amincewa da rahoton Kwamitin Ayyuka na Musamman akan NWDC ya yi. Ƙudirin dokar wanda ya wuce karatu na uku a majalisar ya samu ɗaukar nauyin mataimakin shugaban majalisar dattawa Barau Jibrin, da wasu ’yan majalisa 20 daga jihohi bakwai na shiyyar Arewa maso Yamma. Shugaban kwamitin Sanata Shehu Kaka (mai wakiltar Borno ta tsakiya) wanda ya gabatar da ƙudirin, ya ce an tsara…
Read More
Tsohon lauyan Trump ya ce uban gidansa ya ba ‘yar finafinan batsa toshiyar baki

Tsohon lauyan Trump ya ce uban gidansa ya ba ‘yar finafinan batsa toshiyar baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da ƙara su kai ta fatan ya aikata, na bayar da bayanan da suka tabbatar da tuhume-tuhumen da suka gabatar wa kotu. Shaidar da Cohen, ya bayar dai ta ƙara tabbatar da zargin masu gabatar da ƙara na alaƙar Trump da Stormy Daniels. A baya dai an zargi Trump ɗin da yin lalata da Stormy Daniel, kuma ya biya ta maƙudan kuɗaɗen toshiyar baki, don kar ta fallasa alaƙar da ke tsakaninsu. Zargin da Trump ɗin ya rinƙa musawa a lokutan baya, ko da yake ana ganin yana…
Read More
Ƙungiyoyin Firimiya na neman a soke amfani da na’urar VAR

Ƙungiyoyin Firimiya na neman a soke amfani da na’urar VAR

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyoyin gasar Firimiyar Ingila za su kaɗa ƙuri'ar amincewa ko akasin haka kan cigaba da amfani da na'urar VAR mai taimaka wa alƙalin wasa a wata mai zuwa. Kulob ɗin Wolves ya miƙa ƙudiri a hukumance zuwa ga hukumar firimiya, abin da zai sa a kaɗa ƙuri'ar lokacin da mambobin gasar za su gana ranar 6 ga watan Yuni. Ƙungiyar ta ce an ƙaddamar da VAR ɗin ne da "kyakkyawar manufa" amma kuma ta koma jawo abubuwan da ba a nufata ba da ke lalata alaƙar 'yan kallo da wasan ƙwallon ƙafar". An fara amfani da…
Read More
Gwamnatin Tinubu ta fara watandar rijiyoyin ɗanyen man fetur

Gwamnatin Tinubu ta fara watandar rijiyoyin ɗanyen man fetur

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Kula da Ɗanyen Mai da ake Fitarwa Waje (NUPRC), ta bayyana cewa an fara bayar da lasisin mallakar rijiyoyin mai na shekarar 2024. Shugaban Hukumar NUPRC, Gbenga Komolafe ne ya bayyana haka a Miami, Florida a ƙasar Amurika inda hukumar ta ɗauki nauyin wani nune-nune, tare da haxin-gwiwar Ƙungiyar Masu Fasahar Harkokin Ɗanyen Mai ta Nijeriya (PETAN). Hukumar ta ce rabon lasisin mallakar rijiyoyin ɗanyen mai a 2024 zai shafe tsawon watanni 9. Yayin da Komolafe ya bayyana tandar nema da cancantar mallakar, ya ce tun a ranar 29 ga Afrilu aka yi…
Read More