Editor

9513 Posts
Ministar Mata ta buƙaci dakatar da auren mata marayu 100 a Neja

Ministar Mata ta buƙaci dakatar da auren mata marayu 100 a Neja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ministar Harkokin mata, Uju Kennedy-Ohanenye, ta kai ƙarar Babban Sufeto Janar ’Yan Sandan Nijeriya, Kayode Egbetokun, tare da neman kotu ta dakatar da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkindaji daga aurar ’yan mata marayu 100 a yankin jihar. Amma kakakin ya caccaki ministar saboda "ta wuce gona da iri," yayin da ya sanar da cewa an soke bikin da aka shirya. Matakin da Kennedy-Ohanenye ta bayyana a wani taron ƙara wa juna sani da aka yi a Abuja, wani martani ne ga sanarwar da Sarkindaji ya yi a baya-bayan nan na cewa za a ɗaura…
Read More
Nijeriya ce koma baya a kasafin ilimi a yammacin Afirka – ASUU

Nijeriya ce koma baya a kasafin ilimi a yammacin Afirka – ASUU

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU, ta yi Allah-wadai da yadda ake nuna halin ko-in-kula da harkar ilimi, inda ta ce Nijeriya ce a ƙarshe a kasafin kuɗin ilimi a yankin yammacin Afirka. Shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ne ya bayyana haka a taron yini ɗaya kan ‘Bukatun Ɗalibai masu tasowa a Cibiyoyi’, wanda Asusun Tallafawa Manyan Makarantu (TETFund) ya shirya a Abuja ranar Talata. Ya kuma nanata kiran da ƙungiyar ta yi na sake duba harajin ilimi zuwa kashi 10 cikin 100, yana mai cewa za ta kara kuɗaɗen TETFund daga Naira biliyan 600 a duk shekara…
Read More
Zargin rashawa: EFCC ta sha alwashin ɗaukar mataki kan Matawalle lokacin da ya dace

Zargin rashawa: EFCC ta sha alwashin ɗaukar mataki kan Matawalle lokacin da ya dace

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Kuɗi da Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa, EFCC, ta sake jaddada aniyarta ta gudanar da cikakken bincike kan zargin cin hanci da rashawa da ake yi wa Ƙaramin Ministan tsaro, Bello Matawalle, a lokacin da ya ke Gwamnan Jihar Zamfara. Kakakin hukumar ta EFCC, Dele Oyewale, ya bayyana hakan ne a ranar Larabar da ta gabata, yayin wani taro a hedikwatar EFCC da ke Abuja tare da mambobin ƙungiyar siyasa ta Tinubu Youth and Women Network, da ke fafutukar gudanar da bincike kan zargin almundahana da Matawalle. Ana tuhumar Matawalle…
Read More
ASUU na barazanar shiga yajin aiki bisa rashin kafa majalisun jami’o’i

ASUU na barazanar shiga yajin aiki bisa rashin kafa majalisun jami’o’i

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta bayyana shirin fara yajin aikin gama-gari a faɗin ƙasar domin nuna adawa da gazawar Gwamnatin Nijeriya na kafa Majalisar Gudanarwar Jami’o’in Tarayya. A yayin wani taro da aka yi a sakatariyar ASUU ta ƙasa da ke Abuja, Shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana takaicinsa kan rashin kafa Majalisar Gudanarwa a dukkan jami’o’in tarayya da sauran batutuwan da ba a warware su ba. Farfesa Osodeke ya bayyaba cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta samu isasshen lokaci don magance buƙatun ƙungiyar. A watan Mayun da ya gabata ne gwamnati ta rusa majalisar…
Read More
Nazarin Waƙar ‘Fatima Mai Zogale’

Nazarin Waƙar ‘Fatima Mai Zogale’

Daga ABBA ILIYASU IBRAHIM TSANYAWA Mawaƙi: Alhaji Dauda Abdullahi Kahutu RararaMai Nazari: Abba Iliyasu Ibrahim Tsanyawa. B.A (BUK) Gabatarwa: Waƙar 'Fatima Mai Zogale' da ta ja hankali a Arewacin Najeriya yanzu kuma ta samu shiga fagen nazari, inda wani marubuci kuma mai nazarin adabin baka Abba Iliyasu Ibrahim Tsanyawa ya feɗe waƙar.Kwarjini da karɓuwa da kuma daɗin waƙar da salonta ake ganin ya ja hankalin mutane musamman matasa (maza da mata) da dattawa da sauran masu sha'awar harkokin adabin Hausa wajen tofa albarkacin bakinsu a kan waƙar, a daidai lokacin da ake cikin yanayin zaman tsadar rayuwa a ƙasar tare…
Read More
Yawancin matan sojoji sun dogaro kacokam kan abinda mazajensu ke ba su – Rashida Usman Yahaya

Yawancin matan sojoji sun dogaro kacokam kan abinda mazajensu ke ba su – Rashida Usman Yahaya

"Yaran sojoji suna samun tarbiyya sosai" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ba kasafai ake jin labarin irin rayuwa da gwagwarmayar da matan sojoji da sauran jami'an tsaro masu ɗamara suke gudanarwa a ɓangaren taimakon al'umma da cigaban muhallin da suke rayuwa a ciki ba. Saboda ƙa'idoji da dokokin rayuwar bariki. Amma a yanzu abubuwa sun fara canzawa, wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya samu kutsawa har cikin barikin sojoji na Rukuba da ke Jos, inda ya samu ganawa da Hajiya Rashida Usman Yahaya, wata jajiryacciyar mata mai himma, wacce musamman ta kafa wata gidauniya don ganin ta inganta rayuwar matan…
Read More
Adadin waɗanda suka rasu a harin masallaci a Kano ya ƙaru zuwa 15

Adadin waɗanda suka rasu a harin masallaci a Kano ya ƙaru zuwa 15

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce adadin mutanen da suka mutu a harin da wani matashi ya kai wa wasu masallata a wani masallaci a Kano ya kai mutum 15, Ana zargin cewa matashin ya watsa fetur a masallacin tare da cinna wuta, sannan kuma ya kulle ƙofar masallacin, tare da mutum kusan 40 a ciki. Rahotonnin sun ce matashin ya kai harin ne sakamakon rigima kan rabon gado, Shafi’u Abubakar ya yi zargin mutanen da ya cinna wa wutar mafi yawancinsu suna cikin Masallacin kuma sun cutar da shi a rabon gadon, Tuni…
Read More
Gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin sojoji wajen fatattakar ‘yan ta’adda a Zamfara

Gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin sojoji wajen fatattakar ‘yan ta’adda a Zamfara

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya yaba wa dakarun haɗin gwiwa dangane da sabunta salon yaƙi da 'yan fashin daji a jihar. Sanarwa mai ɗauke da sa hannun kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ta ce, a ƙarshen makon da ya aka tura ƙarin sosjoji jihar domin ci gaba da fatattakar 'yan ta'addan da ke addabar sassan jihar. Sanarwar ta kuma bayyana ƙoƙarin da sojojin ke yi a wannan lokaci na murƙushe 'yan ta'adda a matsayin matakin da ya dace a ɗauka na ganin bayana ɓata-garin a jihar Zamfara. Sanarwar ta ce, “Aikin da sojoji ke yi a yankunan da…
Read More
Kada ku ƙyamaci masu roƙon ku taimaka musu

Kada ku ƙyamaci masu roƙon ku taimaka musu

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Halin ƙuncin rayuwa da yunwa da ake fama da shi a wannan lokaci na koma bayan tattalin arziki da talauci a ƙasa, ya jefa iyalai da magidanta da dama cikin wani mawuyacin rayuwa. Samun damar cin abinci sau uku ko sau biyu a wuni ya fara zama tarihi a wajen wasu. Magidanta da dama sun zama maroƙan ƙarfi da yaji, tun mutum na jin nauyin ya yi roƙo, har ya fara zama masa jiki, don dai neman abin da zai ciyar da iyali, ko da kuwa shi zai haƙura ya kwana da yunwa. Muna sane…
Read More
Hajji 2024: Jirgin farko ya bar Nijeriya ɗauke da maniyyata 422

Hajji 2024: Jirgin farko ya bar Nijeriya ɗauke da maniyyata 422

Yayin da Hajjin bana ya ƙarato, Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), ta fara jigilar maniyyatan bana zuwa ƙasa mai tsarki. A ranar Laraba hukumar ta ƙaddamar da jigilar inda ta fara da maniyyatan jihar Kebbi su 422 da jami'ai 7. Jirgin Flynas mai lamba XY8002 shi ne ya kwashi maniyyatan zuwa birnin Madina da misalin ƙarfe 4:54. Daga adadin naniyyatan, 269 maza ne, sannan 153 mata.
Read More