Editor

9513 Posts
Yajin aiki: Muna nan kan bakanmu – SSANU/NASU

Yajin aiki: Muna nan kan bakanmu – SSANU/NASU

Daga AISHA ASAS Haɗaɗɗen Kwamitin Ƙungiyar Ma'aikatan Jami'o'i (NASU) da kuma Ƙungiyar Manyan Ma'aikatan Jami'o'i (SSANU), ya tsayar da ranar Juma'a (05/02/2021) a matsayin ranar da mambobin ƙungiyoyin biyu za su soma yajin aiki na sai baba-ta-gani sakamakon gazawar da suka ce gwamnati ta yi wajen biya musu buƙatunsu. Tun farko, sai da ƙungiyoyin suka bai wa gwamnati wa'adin makonni kan ta magance musu matsalolinsu ko kuma su tsunduma yajin aiki. Shugaban SSANU Muhammed Haruna, ya shaida wa Manhaja cewa, babu wata yarjejeniya da ƙungiyoyin suka cim ma da gwamnati kan janye ƙudirin shiga yajin aikin. Yana mai cewa, tattaunawar…
Read More
Buhari ya zaɓi tsoffin hafsoshi a matsayin jakadu

Buhari ya zaɓi tsoffin hafsoshi a matsayin jakadu

Daga WAKILIN MU Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa sunayen tsoffin hafsoshin tsaron da suka yi murabus kwanan nan, ga Majalisar Dattawa domin amincewa da naɗa su a matsayin jakadu. A cikin wasiƙar da Buhari ya aika wa Sugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, Buhari ya ce, "Bisa la'akari da Kundin Tsarin Mulki sashe na 171 (1) da sashe na (2) (c) da ƙaramin sashe na (4) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 na Tarayyar Nijeriya wanda aka yi wa gyaran fuska, ina mai gabatar da waɗannan sunaye guda 5 don neman amincewar Majalisar Dattawa kan yi musu naɗin…
Read More
Fulani na da ‘yancin zama ko’ina a Nijeriya – Ƙungiyar Igbo

Fulani na da ‘yancin zama ko’ina a Nijeriya – Ƙungiyar Igbo

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Gamayyar Ma'aikata 'Yan Kudu Maso-gabas a Nijeriya da Ƙetare (CSEPNND), sun yi tir da ayyukan 'yan ƙungiyar IPOB ƙarƙashin jagorancin Nnamdi Kanu, musamman ma la'akari da yadda suke muzguna wa Fulani makiyaya a shiyarsu. A wata takardar bayani da shugaban ƙungiyar, Prof. Madumere Chika, ya fitar a ranar Alhamis wadda Jaridar Manhaja ta samu kwafinta, Chika ya ce Fulani makiyaya na da 'yancin zama ko'ina a faɗin Nijeriya ba tare da fuskantar muzgunawa ba kamar dai yadda Kundin Dokokin Ƙasa na 1999 ya nuna. Ƙungiyar ta cacciki Kanu da mabiyansa kan cewa sun sa ana yi…
Read More
NCDC ta samar da lambar tantance sahihancin bayanai

NCDC ta samar da lambar tantance sahihancin bayanai

Daga AISHA ASAS A matsayin wani mataki na sauƙaƙa wa 'yan Nijeriya iya tantance sahihancin bayanai game da cutar korona, Cibiyar Daƙile Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Ƙasa (NCDC) tare da taimakon Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), ta samar da lamba ta musamman da za ya taimaka wa 'yan ƙasa wajen tantance bayanai. NCDC ta ce, a duk lokacin da buƙatar neman tabbatar da sahihancin wani bayani ta taso, 'yan ƙasa na iya kiran lambar “6232” don tabbatar da ingancin wani bayani a kan korona da sauran cututtuka. A bayanin da Babban Daraktan NCDC, Dr Chikwe Ihekweazu, ya yi a Larabar…
Read More
Shirin kula da ilimin yara milyan 6.9 ya kankama – inji Gwamnatin Tarayya

Shirin kula da ilimin yara milyan 6.9 ya kankama – inji Gwamnatin Tarayya

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta sanar cewa, ta soma gudanar da shirinta na neman bai wa yaran da suka daina zuwa makaranta ilimi a faɗin ƙasa. Sanarwar hakan ta bayyana ne a shafin tuwita na Shugaban Ƙasa a Larabar da ta gabata. Idan dai za a iya tunawa, a Janairun da ya gabata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya kafa wani kwamiti na musamman mai mambobi 18 tare da ɗora masa nauyin kula da wannan shiri, ƙarƙashin jagorancin Ministar Jinƙai da Agaji da kuma Ministan Ilimi. Buhari ya ce, shirin zai maida hankali ne wajen karantar da yara darussan Lissafi…
Read More
Gwamnati ta amince da batun buɗe sabbin jami’o’i 20 a faɗin ƙasa

Gwamnati ta amince da batun buɗe sabbin jami’o’i 20 a faɗin ƙasa

Daga AISHA ASAS Majalisar Zartarwa ta Tarayya, ta aminta da batun samar da sabbin jami'o'i masu zaman kansu guda 20 a faɗin ƙasa. Majalisar ta cim ma wannan matsaya ne yayin zamanta na Larabar da ta gabata ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu ya ce, jami'o'in za su samu lasisin zarafin gudanarwa ne daga hannun Hukumar Kula da Jami'o'i ta Ƙasa (NUC), wanda za su yi amfani da shi nan da shekaru uku masu zuwa, yayin da gwamnati za ta ci gaba da sanya musu ido. Jami'o'in da Majalisar ta amince da a kafa ɗin…
Read More
Myanmar: An maka Suu Kyi a kotu

Myanmar: An maka Suu Kyi a kotu

Daga FATUHU MUSTAPHA Rahotanni daga ƙasar Myanmar sun tabbatar da cewa an gurfanar da jagorar Myanmar, Aung San Suu Kyi gaban kotu a Larabar da t gabata, kwanaki biyu bayan tsare ta da sojojin da suka kifar da gwamnatin ƙasar suka yi. Kazalika, bayanai sun ce, kiraye-kirayen tada ƙayar baya don nuna adawa da juyin mulkin ƙasar sai ƙaruwa suke. Ƙasar Myanmar da ke Kudu maso gabashin nahiyar Asiya ta sake faɗawa cikin mulkin soji ne bayan da wasu gungun sojoji suka damƙe jagororin mulkin farar hula a Litinin da ta gabata, lamarin da ya kawo ƙarshen mulkin dimokraɗiyyar ƙasar…
Read More
Ronaldo ya kafa sabon tarihi bayan zira ƙwallaye 763 a raga

Ronaldo ya kafa sabon tarihi bayan zira ƙwallaye 763 a raga

Daga UMAR M. GOMBE A halin da ake ciki, Cristiano Ronaldo ya zama kan gaba a tarihin duniyar ƙwallon kafa a matsayin wanda ya fi kowane ɗan wasan yawan zira ƙwallo a raga. A cewar Marca, Ronaldo wanda dan asalin ƙasar Portugal ne, ya taki wannan matsayi ne a karawar da ƙungiyarsu ta yi da Inter Milan a daren da ya gabata a wasan kusa da na ƙarshe na cin kofin Italiya. Yadda al’amarin yake yanzu, Ronaldo ya ci ƙwallaye guda 763 a matsayinsa na dan ƙwallo, wanda hakan ya zarce na marigayi Josef Bican da Pele, wanda kowannensu ya…
Read More
Haɗin kan Neja da Kaduna abin yabo ne – El-Rufai

Haɗin kan Neja da Kaduna abin yabo ne – El-Rufai

Daga BASHIR ISAH Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya yaba wa takwaransa na jihar Neja, Abubakar Sani Bello, bisa haɗa kai da Kaduna wajen yaƙi da harkokin masu sace-sacen mutane a iyakokin Kaduna da Neja. El-Rufai ya yi wannan yabo ne yayin ziyarar da ya kai wa Gwamna Bello a Minna, babban birnin jihar. Babbar Sakatariyar Yaɗa Labarai ta gwamnan Neja, Mary Noel-Berje ta ce, El-Rufai ya yi ziyarar ne domin jajanta wa gwamnati da ma al'ummar jihar game da rashin wani fitaccen ɗan jihar da ya auku ba da daɗewa ba. Yayin ziyar, Gwamana El-Rufai ya ce, Neja…
Read More
Masu garkuwa da mutane sun shata daga a junan su: Sama da mutum ɗari sun mutu

Masu garkuwa da mutane sun shata daga a junan su: Sama da mutum ɗari sun mutu

Daga FATUHU MUSTAPHA A ranar Alhamis da misalin ƙarfe 5 na yamma ne wani gungun masu garkuwa da mutane suka nemi kutsa kai cikin garin Illela na Ƙaramar Hukumar Safana da ke Jihar Katsina. Wannan kutse ya janyo musayar wuta tsakanin su da wani gungun masu garkuwa da mutanen, inda ya yi sanadiyar mutuwar sama da mutum ɗari, ciki kuwa har da mata da yara ƙanana. Rahotanni sun bayyana cewa wannan rikici ya faru ne tsakanin gungun Mani sarki da na Ɗanƙarami wanda ke da goyon bayan Gungun Abu Rada. Shi dai Sarki Mani wanda a da tsohon mai garkuwa…
Read More