01
Aug
Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Aƙalla mutane 19 ne su ka rasa rayukansu a yayin fashewar wani bom da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne su ka dasa a wajen cin abinci a ƙauyen Kawuri da ke ƙaramar hukumar Konduga a jihar Borno. Lamarin, ya auku ne a ranar Laraba, kwanaki bayan da mayaƙan su ka kai hari ofishin ƴan sandan Jakana da ke ƙaramar hukumar inda aka kashe ɗan sanda da wata mata tare da ƙona motocin sintiri guda biyu. Wani jami'in gwamnati daga ƙauyen, ya ce lamarin ya auku ne da misalin ƙarfe 8:50 na dare inda mutane ke…
