Babaji

4790 Posts

Zanga-zanga: Amurka, Birtaniya da Canada sun gargaɗi al’umma kan tsaro

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƙasashen Amurka, Birtaniya da Canada sun ankarar da al'ummar Nijeriya game yiwuwar aukuwar tashin-tashina yayin zanga-zangar tsadar rayuwa da za a fara a ranar Alhamis. Ƙasashen sun aika sakonnin ne ta mabanbanta hanyoyi inda su ka gargaɗi mutanensu da su ƙaurace wa artabu da ka iya aukuwa tsakanin jami'an tsaro da ƴan zanga-zanga, su na masu bada misali da ire-iren yadda su ka faru a baya. Sannan, saƙonnin sun iso ne bayan da manyan ƴan kasuwa a jihohin Abuja, Sakkwato, Kano, Katsina, Ogun, Osun, Zamfara, Gombe da wasu yankunan Nijeriya su ka buƙaci a tsaurara tsaro…
Read More

Da Ɗumi-Ɗumi: Majalisa ta kira taron gaggawa kan zanga-zanga

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shugaban Majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ya kira taron gaggawa na ƴan Majalisar. Sanarwar kiran ta fito daga ofishin akawonsa, Chinedu Akubueze a ranar Litinin inda ya ce za a yi taron ne musamman kan ababan da ke damun ƙasa a halin yanzu. Za a gudanar da taron ne a ranar Laraba, 31 ga watan Yuli, 2024 da misalin ƙarfe 12 na rana, kwana ɗaya kafin fara zanga-zangar tsadar rayuwa a faɗin Nijeriya. Sanarwar ta ƙara da cewa, ana buƙatar sanatoci su yi duk shirye-shiryen da su ka dace don tattauna batutuwa masu muhimmanci ga ƙasa, majalisar…
Read More

Zanga-zanga: Ku tabbatar da tsaro a makarantu, Gwamnatin Tarayya ga shugabannin jami’o’i

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Yayin da ake cigaba da kusantar kwanakin zanga-zangar tsadar rayuwa a faɗin Nijeriya, Ministan Ilimi, Tahir Mamman, ya umarci shugabannin jami'o'i su shirya matakan kariya don bai wa makarantunsu da malamai da ɗalibai tsaro a lokacin zanga-zangar. Sakataren hukumar kula da jami'o'i ta Ƙasa (NUC), Chris Maiyaki ya fitar da wata sanarwa a ranar Litinin, ya na mai umartar shugabannin jami'o'i su fitar da jawabai na tabbatar da tsaro ga malamai da ɗaliban makarantunsu. Maiyaki, ya kuma shawarci ɗalibai da su kasance a cikin makarantu tare da mayar da hankali kan karatunsu domin kauce wa haɗuran…
Read More

Sojoji sun karɓe ragamar kula da manyan titinan Abuja kwana uku kafin zanga-zanga

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI An samu matsewar ababan hawa a babbar hanyar Keffi-Abuja yayin da jami'an soji su ka datse wani yanki domin gudanar da bincike kafin shiga Birnin Tarayyar Abuja. Sojojin sun tare daidai barikin sojoji na Abacha da ke kusa da shataletalen AYA. Kasancewar hukumomin tsaro ba su bada sanarwar hakan ba, an samu cinkoson ababan hawa wanda ya kai har gadar Nyanya, kilomita 12 kafin wajen da aka datse. Da dama daga cikin ma'aikata da ƙananan ƴan kasuwa na Abuja da ke zama a Nyanya, Maraba, Karu da Masaka, an tilasta mu su komawa gida bayan tsawon…
Read More

‘Yan bindiga sun kai hari sansanin hukumar Kwastom, sun kashe jami’i da garkuwa da wani

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƴan bindiga sun kashe jami'in Kwastom tare da yin garkuwa da wani a harin da su ka kai sansanin hukumar a yankin Koko/Besse da ke Jihar Kebbi. Jami'in hulɗa da jama'a na hukumar a Jihar, Tajuddeen Salisu ya ce al'amarin ya faru ne a ranar Alhamis. Ya bayyana cewa, bayan garkuwa da ɗaya jami'in, ƴan bindigar sun kuma buƙaci maƙudan kuɗaɗe domin sako shi. Ya ƙara da cewa, an karɓi gawar jami'in da aka kashe shi ta hanyar yanka tare da kai shi Jihar Kaduna domin yi masa jana'iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar. Kazalika,…
Read More

Da ƊUMI-ƊUMI: Zanga-zangar yunwa ta ɓarke a Neja

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Wasu matasa a Jihar Neja sun fito cikin gari domin zanga-zangar tsadar rayuwa da ake fama da shi a Nijeriya. Matasan sun fito da alluna da ke ɗauke da batutuwa kamar haka; 'Enough is Enough', Stop 'Anti-Masses Policies', 'We Are Not Slaves In Our Country', 'Hardship Is Unbearable', 'Fuel Subsidy Must Be Back' da sauransu. A lokacin zagayen, matasan na rera wakokin da ke nuna adawa da gwamnati. Gwamnatin Tarayya da na jihohi sun yi ta ƙoƙarin dakatar da zanga-zangar saboda kar ɓata-gari su yi amfani da shi wajen haddasa fitina a ƙasa daga waɗanda ke…
Read More

Yadda farashin man fetur ya kai N1,300 a jihohi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Sakamakon bushewa da rijiyoyin man fetur da dama su ka yi, an samu layuka a gidajen mai a jihohin Kano, Legas, Kaduna, Ribas, wasu yankuna na Abuja, Nija da wasu jihohi a faɗin Nijeriya. Rahotanni sun bayyana cewa, hakan ya sa ƴan bunburutu su ke amfani da damarsu wajen sayar da duk lita ɗaya a farashin N1,300 da N1,500 a jihohin Legas da Ogun. An fara samun yawaitar layin man ne tun ranar Asabar a jihohin inda kamfanin man fetur na Ƙasa, NNPC ya ce hakan na faruwa ne sakamakon tseko da ake samu wajen ɗakko…
Read More

Ba yaudara a rarrashin da Tinubu ke yi kan zanga-zanga – Sanata Barau

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Barau I. Jibrin ya roƙi masu shirya zanga-zangar gama-gari su sake yin nazari kan hukuncinsu tare da janye wa daga batun, don kar a yamutsa sauran zaman lafiyar da ya rage wa Nijeriya. Barau, wanda shi ne Mataimankin Kakakin Majalisar ECOWAS na farko, ya ce Tinubu na muhimmin ƙoƙari wajen ganin an magance matsalolin Nijeriya. Wata takarda da ta fito daga ofishin mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ismail Mudashir, ta ce Barau ya yi kira ga masu hura wutar zanga-zangar kan cewa su bai wa Shugaba Tinubu ƙarin…
Read More

Ku nisanci zanga-zanga, inji jagoran CAN ga Kiristoci

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƙungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) reshen jihar Nija ta yi kira ga mabiyanta cewa kar su shiga zanga-zangar tsadar rayuwa da za a yi a watan Agusta. Shugaban CAN na jihar, 'Bishop Bulus Yohanna ya faɗi hakan cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ne cewa wasu kan iya amfani da zanga-zangar wajen tada fitina da za ta iya shafar waɗanda basu-ji-ba basu-gani-ba. Yohanna ya kuma yi kira ga Shugaba Tinubu da cewa, baya ga rarraba tallafi, akwai buƙatar a yi aiki kan farashin kayayyaki wanda hakan ya haifar da tsadar rayuwa ƙasar da kuma batun da…
Read More

Peter Obi ya yi gargaɗi kan ɓarkewar rikici a zanga-zanga

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2023, Peter Obi ya bayyana matsayarsa game da zanga-zangar tsadar rayuwa da ke tafe A wata Agusta. A lokacin da ya ke magana bayan wani zama da gwamnan Jihar Abia, Alex Otti a ranar Lahadi, Obi ya ce masu zanga-zangar sai sun tabbatar da kiyaye doka da oda, ya na mai kira ga hukumomin tsaro cewa su bi umarnin doka, domin duk duniya an halatta yin zanga-zanga. Wannan shi ne karo na farko da Obi ya magantu kan zanga-zangar. Mai bai wa Shugaba Tinubu shawara kan harkokin labaru, Bayo…
Read More