03
Jul
Daga USMAN NASIR KAROFI a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan Kabir Yusuf, wanda ya rasu ranar Talata. Bayanin hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, a yau Laraba. Sanarwa ta ce, “Yusuf ƙwararren ɗan jarida ne, wanda ya kasance manemin labarai na Birnin Tarayya na Jaridun The Triumph da kuma Radio France Internationale Hausa. “Ya yi wakilin Fadar Shugaban Ƙasa na jaridu da dama tsawon shekaru da dama har zuwa rasuwarsa. “Shugaba ya yi addu'ar Allah ya jikan sa, kuma ya ba iyalansa hakuri a…
