ukarofi

11627 Posts
Ana cece-kuce kan rufta Nijeriya yarjejeniyar auren jinsi

Ana cece-kuce kan rufta Nijeriya yarjejeniyar auren jinsi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wasu malamai sun koka akan Gwamnatin Tarayya, domin sanya hannu akan yarjejeniyar nan mai cece-kuce ta Samoa, wacce ake zargin ta na ƙunshe da amincewa da tsarin auren jinsi. A cewarsu, yarjejeniyar tana ɗauke da wasu sharaɗai da suka ƙunshi cewa ƙasashe masu tasowa dole su yarda da ’yancin ’yan luwadi da ’yan maɗigo da kuma ’yancin yin auren jinsi ɗaya. Yarjejeniyar an samar da ita a tsibirin Samoa, inda aka sanya ma ta hannu a ranar 15 ga Nuwamba, 2023, amma tun lokacin yarjejeniyar ke samun suka daga addinai da dama, saboda hakan…
Read More
Binciken Ganduje: Kotu ta ba shugabannin kwamiti kwana biyu su sauka

Binciken Ganduje: Kotu ta ba shugabannin kwamiti kwana biyu su sauka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta umarci alƙalan babbar kotun  jihar, Mai Shari’a Faruk Lawal Adamu da Mai Shari’a Zuwaira Yusuf, wa’adin awa 48 su sauka daga shugabancin kwamitocin binciken da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa domin bincikar tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje. Alƙalan biyu ne ke jagorantar kwamitoci biyu da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa don bincikar Gwamnatin Ganduje kan zargin karkatar da kuɗaɗe da kadarorin gwamnati da kuma kwamitin bincike kan rikicin siyasa da ɓacewar mutane daga 2015 zuwa 2023. Mai Shari’a Simon Amobeda, ya umarci Hukumar Kula da…
Read More
Majalisa na aiki don tabbatar da ’yancin ƙananan hukumomi da masarautu – Abbas

Majalisa na aiki don tabbatar da ’yancin ƙananan hukumomi da masarautu – Abbas

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, ya ce, Majalisa ta 10 a ƙarƙashin jagorancinsa ta ɗauki matakai da nufin tabbatar da ayyukan da tsarin mulki ya amince da su ga masarautun gargajiya da kuma cin gashin kan ƙananan hukumomi a Nijeriya. Shugaban Majalisar, wanda ya bayyana hakan a wajen bikin kwana biyu na ‘taron mako’ da ake yi na murnar cika shekaru 10 da kafuwar Majalisar ta 10, ya ce, a cigaba da manufofin majalisar na kafa wasu kwamitoci na musamman guda biyu da za su tafiyar da aikin na aiwatar da ’yancin…
Read More
Dole masu POS su yi rijista kafin ƙarewar wa’adi – Hukumar CAC

Dole masu POS su yi rijista kafin ƙarewar wa’adi – Hukumar CAC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gabanin cikar wa’adin yin rajistar kasuwanci na dole tare da Hukumar Kula da Kamfanoni ta Nijeriya, CAC, Jakadan Hukumar, Michael Nwabufo, ya buƙaci masu sana'ar POS da masu ƙananan sana’o’i su gaggauta yin rajista da hukumar. Nwabufo, manajan tallar hukumar, ya jaddada a cikin wata sanarwa da ya fitar kwanan nan a Legas cewa dole ne masu POS su guje wa rikice-rikice ta hanyar tabbatar da rajistar su kafin wa'adin. Da yake ƙarin haske kan mihimmancin wa'adin, wanda ya rage saura kwanaki biyar, Nwabufo ya ƙarfafa 'yan kasuwa da su yi amfani da manhajar CAC Special…
Read More
Jam’iyyar Labour ta lashe  zaɓen Ingila yayin da gwamnatin Conservative ta faɗi warwas

Jam’iyyar Labour ta lashe zaɓen Ingila yayin da gwamnatin Conservative ta faɗi warwas

Jam'iyyar Labour tayi nasarar samun kujeru 326 a zaɓen Ingila, wanda hakan na nufin itace zata kafa gwamnati, wanda Keir Starmer zai zama Firayim minista. Wanda Jam'iyyar ta conservative ta samu nasarar kujeru 58, wanda hakan na nufin, ta samu kaso 21.1% na zaɓen. Sai Liberal Democracy sun samu, kaso 10.6% na zaɓen, green party da SNP duk suma sun samu kaso kaɗan daga cikin zaɓen. Ministoci takwas sun rasa kujerun su a wannan babban zaɓen, wanda haka ya karya tarihi da ake dashi na shekarar 1997 wanda ministoci bakwai suka rasa kujerun su. Tuni dai Firayim Minista na yanzu…
Read More
Trump ya sako Kamala Harris a gaba bayan yiwuwar ta maye gurbin Biden a zaɓen 2024

Trump ya sako Kamala Harris a gaba bayan yiwuwar ta maye gurbin Biden a zaɓen 2024

Gangamin yaƙin neman zaɓen Donald Trump da wasu daga cikin abokansa sun fara riga-kafin siyasa kan mataimakiyar shugaban ƙasa Kamala Harris, inda suka yi gaggawar ƙoqarin ɓata mata suna a yayin da wasu ‘yan jam’iyyar Democrats suka yi hasashen cewa za ta maye gurbin shugaban ƙasa Joe Biden a saman tikitin takarar shugaban ƙasa na 2024. A shafukan sada zumunta da kuma wasu kalamai da aka yi ta yi a tsakanin awowi 48 da suka gabata, da alama yaƙin neman zaɓen Trump da 'yan jam'iyyarsa na Republican suna shimfiɗa harsashin kai hari kan Harris idan Biden mai shekaru 81 ya…
Read More
Kotu ta rushe zaɓen fidda gwani na PDP a Jihar Edo

Kotu ta rushe zaɓen fidda gwani na PDP a Jihar Edo

Mai shari'a Inyang Ekwo na babbar kotun take ƙasa ya rushe zaɓen fidda gwani na jam'iyyar PDP da ya ba Asue Ighodala nasara. Zaɓen fidda gwanin wanda akayi 22 ga watan Fabarairu 2024 babu shi inji mai shari'a Ekwo. Ya bada dalilin hakan ne sabida masu Zaɓen cikin gida wato delegates guda 378 da yakamata suyi zaɓe ba a basu dama ba. Sauran bayanai na zuwa…
Read More
Mutum biyu sun mutu a faɗan manoma da makiyaya a Jigawa

Mutum biyu sun mutu a faɗan manoma da makiyaya a Jigawa

'Ƴan sandan Jihar Jigawa sun tabbatar da faruwar wani rikici tsakanin manoma da makiyaya. Abun ya faru ne a ƙaramar hukumar Birnin Kudu, wanda yayi sanadiyar mutuwar mutum biyu da ƙona gidaje uku. Shaidun gani da ido sun shaida cewa, wasu makiyaya sun gayyato makiyaya daga Jihar Katsina, wanda hakan yayi sanadiyar dabbobin su ke shiga gonaki suna yin ɓarna. Wannan ne yasa manoman su kayi ganganmi domin kare gonakin su. Mai magana da yawun yan sandan Jihar Jigawa, DSP Lawan Shiisu Adam ya bayyana cewa, yanzu haka yan sanda, da bigilanti, da sibil defens sun yi kokarin kawo lumana…
Read More
Auren jinsi: Nijeriya ta sanya hannu kan Yarjejeniyar Samoa

Auren jinsi: Nijeriya ta sanya hannu kan Yarjejeniyar Samoa

Wasu malamai sun koka akan gwamnatin tarayya domin sanya hannu akan Yarjejeniyar nan mai cece kuce ta Samoa. A cewar su, Yarjejeniyar tana ɗauke da wasu sharaɗai da suka ƙunshi cewa ƙasashe masu tasowa dole su yarda da yancin, yan luwadi, da yan maɗigo da yancin masu auren jinsi ɗaya. Yarjejeniyar an samar da ita a tsibirin Samoa, nan aka sanya hannu a 15 ga watan Nuwamba 2023. Amma tun lokacin Yarjejeniyar ke samun suka daga addinai da dama wanda hakan ya saɓawa al'adunsu. Bayanai akan Yarjejeniyar ya fito ne lokacin da ministan kasafin kuɗi da tattalin arziki Alhaji Abubakar…
Read More
Matsayin gara a mahangar magabata

Matsayin gara a mahangar magabata

Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin iyali na jaridar Blueprint Manhaja. Muna godiya da bibiyar mu da ku ke yi. A wannan makon za mu tattauna ne kan tasirin gara a aure, da kuma matsayin da take da shi ga al'ummar Ƙasar Hausa, da kuma bayanai kan matsayin gara a aure a mahanga ta magabata. Idan muka yi maganar gara a nan muna magana ne kan kayan da ake kai wa gidan wanda aka aura bayan an kai amarya a matsayin tukuici ko nuna isa ko nuna ƙimar ɗiyar da danginta suka bada auren nata.…
Read More