22
Jun
Daga MAHD MM. MUHAMMAD Wata Kotun Majistare da ke Abeokuta, reshen Isabo, a ranar Laraba, ta bayar da umarnin tsare wata mata ’yar shekara 25 bisa zargin ta da yi wa wata yarinya 'yar shekara 12 mummunar azaba da wuta ta hanyar ɗaɗara mata a al’aurarta. Wadda ake tuhumar wadda ke zaune a lamba 6 Isewo Dotin a unguwar Obada-Oko a Abeokuta, tana fuskantar tuhuma guda ɗaya da laifin haddasa mummunar ɓarna. Wadda ake tuhumar ta amsa laifin da ake tuhumarta da aikatawa tare da roƙon gafarar kotun. Alƙalin kotun, B.Ɓ. William, ta bada umarnin tsare ta a gidan gyaran…
