Rahotanni daga jihar Neja, sun tabbatar da ‘yan bindiga sun sako ɗaliban makarantar Islamiyyar Salihu Tanko su 70 da aka yi garkuwa da su a garin Tegina.
Sakin nasu na zuwa ne bayan da suka shafe kwanaki 88 a hannun ‘yan bindigar.
Ya zuwa lokacin haɗa wannan labari, an ce ɗaliban suna hanyarsu ta zuwa Minna daga Kagara.
Tun farko sai da aka biya ‘yan bindigar Naira miliyan N50 a matsayin kuɗin fansa don dai a samu su sako yaran amma suka ƙi amincewa.
An yi garkuwa da ɗaliban ne su 156 daga Islamiyyar a ranar Litinin, 30 ga Mayun da ya gabata, bayan da ɗaruruwan ‘yan bindiga suka yi wa garin dirar mikiya lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutum guda a wancan lokaci.
A watan Yuni ne ɓarayin suka buƙaci a biya su fansar milyan N200 kafin su sako ɗaliban.
Daga baya ne da iyayen yara suka ga wankin hula na neman ya kai gwamnati dare, suka yanke shawarar neman taimako a masallatai da mujami’u don tara kuɗin da za su yi amfani da shi wajen ceto yaransu.