Nishadi

Yadda faɗuwar Peter Obi ta hana jarumi Kanayo O. Kanayo bikin zagayowar ranar haihuwar sa

Yadda faɗuwar Peter Obi ta hana jarumi Kanayo O. Kanayo bikin zagayowar ranar haihuwar sa

Daga AISHA ASAS Sanannen jarumi a masana'antar finafinai ta Kudu, wato Nollywood, Kanayo O. Kanayo, ya bayyana tsabar baƙin cikin sa kan yadda Peter Obi bai amshi mulkin ƙasar nan a zaɓen da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023. Jarumin ya bayyana lamarin a matsayin abin kunya, sakamakon yana layin waɗanda suke iqirarin an yi murɗiya a zaɓen, domin Peter Obi, na Jam'iyyar LP ne ya samu quri'u mafi rinjaye. Kanayo ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a jiya, wanda ya yi daidai da ranar mauludin haihuwarsa cewa, zuciyarsa cike ta ke da ɓacin rai duk…
Read More
Na sha wahala a fim ɗin ‘Farida Nabil’ – Haruna Talle Maifata

Na sha wahala a fim ɗin ‘Farida Nabil’ – Haruna Talle Maifata

Daga IBRAHIM HAMISU Haruna Talle Maifata wani fitaccen jarumin ne da ya yi fice a masana'atar fim ta Kannywood, inda ya fi fitowa a matsayin ɗan daba ko mugu, a tattaunawarsa da Ibrahim Hamisu a Jos, za ku ji dalilan da ya sa ya ke fitowa a mugu da kuma irin nasarorin da ya samu a masana'atar. ku biyo mu: MANHAJA: Ko za ka gabatar mana da kanka ga masu karatunmu? HARUNA: Da farko dai ni sunana Haruna Talle maifata. Za mu so jin taƙaitaccen tarihinka? An haifeni a Jos ta Jihar Plateau, na yi karatun primary da secondary, sannan…
Read More
Apama ya karya azumin sa kan zancen fasfon Amurka da ya mallaka

Apama ya karya azumin sa kan zancen fasfon Amurka da ya mallaka

Daga AISHA ASAS Shahararren ɗan wasan barkwanci Dike Osinachi, wanda aka fi sani da Apama Egbeigwe ya magantu kan yadda mutane suka juya bidiyon da ya sake kan sha'anin mallakar fasfon Ƙasar Amurka da ya yi, bayan tsayin lokaci da ya ɗauka bai tanka 'yan gutsiri-tsoma kan zancen. A makwanin baya ne Apama ya wallafa wani faifan bidiyo, inda ya nuna cikin alfahari cewa, ya mallaki shedar izinin zama ɗan ƙasa na Amurka, ta hanyar nuna fasfon Ƙasar Amurka da ya ce ya mallaka tare da na gida Nijeriya. Wanda ya nuna cewa, yanzu shi mazauni Ƙasar Amurka ne kamar…
Read More
Tsohon ɗan wasan shirin BBNaija ya bayyana kwaɗayinsa na son ɗarewa kujerar maigabatar da shirin

Tsohon ɗan wasan shirin BBNaija ya bayyana kwaɗayinsa na son ɗarewa kujerar maigabatar da shirin

Daga AISHA ASAS Sanannen tsohon ɗan wasa a shahararren shirin nan mai farin jini na Big Brother Naija, Adekunle Olopade, ya bayyana kwaɗayin sa na zama magajin mai gabatar da shirin, wato Ebuka Obi Uchendu, idan buƙatar sauya shi ta taso a nan gaba. Adekunle ya yi wannan roƙo ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na Twitter, a ranar Litinin ɗin da ta gabata. Matashin mai kimanin shekaru ashirin da bakwai a duniya, ya yi amfani da kafar sada zumunta ta Twitter ne don aika ƙoƙon barar nasa ga waɗanda abin ya shafa, ta hanyar yaɗa saƙon nasa…
Read More
Maryam Yahaya ƙanwata ce ba soyayya muke ba – Jarumi Shamsu Ɗan’iya

Maryam Yahaya ƙanwata ce ba soyayya muke ba – Jarumi Shamsu Ɗan’iya

Daga IBRAHIM HAMISU, Kano Fitaccen jarumi a masana'atar Kannywood, wato Shamsu Ɗan'iya ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa dangane da cewa wai zai auri Maryam Yahaya. A yan kwanakin nan kafafen sada zumumta na Social Media da wasu Jaridun ƙasar nan sun ta yayata cewa Shamsu Ɗan'iya zai angoce da Jaruma Maryam Yahaya. Shamsu Ɗan'iya da a yanzu aka fi kira da Hisham, ya ce daga lokacin da aka fara yaɗa jita-jitar zuwa yanzu a kodayaushe yana karva kira daga wajen mutane daban-dadan. A wata tattaunawa da ya yi da jaridar Blueprint Manhaja, Ɗan'iya ya ce abin ya samo asali…
Read More
Ina ɗauke da cutar da mutane ƙalilan ne suka taɓa yin ta a duniya – celine Dion

Ina ɗauke da cutar da mutane ƙalilan ne suka taɓa yin ta a duniya – celine Dion

"Cutar ta taɓa damar da nake da ita ta sarrafa muryata zuwa waƙa" Daga AISHA ASAS Rayuwa tamkar karatun boko ce, za ka fara tun daga lokacin da ka ke naziri, zuwa firamare, har ka kai sakandare, daga ƙarshe ka dira jami'a, inda duk wani karatun ƙarshe ta ke cibiyarsa. Duk wannan tafiyar idan ka yi ta, ba za ka iya dawowa baya ba, ma'ana ba zai yiwu kana jami'a ka dawo firamare ba, yin hakan zai sa a yi ma kallon mai tavin hankali. Wannan shi ne ƙaramin misali akan rayuwa, duk ƙurciyarka wata rana za ka girma, kuma…
Read More
EFCC ta cika hannu da ‘yar Nollywood kan wulaƙanta sabbin takardun Naira

EFCC ta cika hannu da ‘yar Nollywood kan wulaƙanta sabbin takardun Naira

Daga BASHIR ISAH Jami’an Hukumar Yaƙi da Rashawa (EFCC) na shiyyar Legas sun fara binciken Oluwadarasimi Omoseyin wadda ‘yar fim ce a masana’antar Nollywood bisa zargin yin facaka da wulaƙanta sabbin takardun Naira. EFCC ta ce abin da wadda ake zargin ta aikata ya saɓa wa Sashe na 21 (5) Dokar Babban Bankin Nijeriya (CBN) na 2007. Mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren, ya ce an tsare Omoseyin ne a ranar Laraba a yankin Ikoyi, Jihar Legas. Kamen nata ya biyo bayan bidiyon da aka yaɗa mai ɗauke da yadda take facaka da sabbin takardun Naira da tattaka su…
Read More
Yawan zance a kafafen sada zumunta ne matsalar Kannywood da ke buƙatar gyara – Shamsu Ɗan Iya

Yawan zance a kafafen sada zumunta ne matsalar Kannywood da ke buƙatar gyara – Shamsu Ɗan Iya

"Ba zan tava mantawa da fim ɗin 'Kar Ki Manta da Ni' ba" Daga IBRAHIM HAMISU, Kano Shamsu Nasir wanda a duniyar Kannywood aka fi sani da Shamsu Dan' iya, jarumi ne da ya fito a cikin finafinai masu ɗimbin yawa, daga ciki akwai wani fitaccen fim mai dogon zango 'Alaƙa' wanda mai gidansa Ali Nuhu yake shiryawa, A tattaunawar sa da Ibrahim Hamisu a Kano, za ku ji nasarori da kuma tarihinsa a cikin shekara 14 da shigarsa cikin Kannywood. Ku biyo mu: MANHAJA: Ko za ka gabatar mana da kanka? SHAMSU: Sunana Shamsu Nasir Ɗan'iya da aka fi…
Read More
Yadda mutuwar Jarumi Kamal Aboki ke shirin sauya akalar rayuwar matasa

Yadda mutuwar Jarumi Kamal Aboki ke shirin sauya akalar rayuwar matasa

Daga AISHA ASAS A ranar Litinin, 16 ga wannan watan ne labarin mutuwar jarumin barkwanci Kamal Aboki ta yi dirar mikiya a tsakanin kafefen sada zumunta da kuma masana'antar fim ta Kannywood, sakamakon kasancewar mutuwar ta fuju'a, wato ba-zata. An ruwaito cewa, Kamal ya mutu ne sakamakon hatsarin mota da ya yi a hanyar Maiduguri zuwa Kano. Wannan mutuwa ta matashi Kamal Aboki da ke tsaka da cin gajiyar lokacinsa ta ɗaga hankalin 'yan ciki da wajen masana'antar Kannywood. Za ka amince da hakan idan ka yi duba da yadda kafafen sada zumunta irin su Facebook, Instagram da kuma TikTok…
Read More
Netflix ya tafka asarar miliyan N250 saboda dakatar da amfani da ‘Naira Card’ da bankuna suka yi

Netflix ya tafka asarar miliyan N250 saboda dakatar da amfani da ‘Naira Card’ da bankuna suka yi

Daga WAKILINMU Kamfanin Netflix ya ce ya rasa mabiya 39,451 cikin kwana 40 a Nijeriya sakamakon daina amfani da katin hada-hadar kuɗi na 'Naira Card' da bankuna suka yi a kasar. Bayanan da jaridar News Point Nigeria ta tattara ranar Talata su nuna cewa, kimanin 'yan Nijeriya mabiya shafin kamfani su 39,000 ba su sabunta rijistarsu da kafar ba a tsakanin kwana 40 da suka shuɗe. Jaridar ta ƙara da cewa, bayanan da ta samu ɗin ba su nuna yadda tsarin yake dalla-dalla ba, kawai dai an hasashen cewa asarar ta kai ta sama da Naira miliyan 250. News Point…
Read More