Nishadi

Da yawan mawaƙan Arewa ba su san yadda za su amfana da basirarsu ba – Haidar Blog

Da yawan mawaƙan Arewa ba su san yadda za su amfana da basirarsu ba – Haidar Blog

"'Diwani' ce bakandamiya a waƙoƙin da na yi" Daga: ADAMU YUSUF INDABO, Kano Fasihin mawaƙin Hausa, kuma ɗan kasuwar da ke dillancin waƙoƙin Hausa a yanar gizo, mai suna Aliyu Abubakar, da ake wa laƙabi da Haidar Blog, ya bayyana wannan kyakkyawan fata da buri da yake da shi ne a kan mawaƙa da dukkan waɗanda Allah Ya yi wa baiwar basirar na suna amfanuwa da basirar tasu don ƙara samun kwarin gwiwa gare su. Tare kuma da yin kira ga matasa da su ƙara ƙaimi wajen neman ilimi, wanda da shi ne rayuwar bawa take yin haske kuma komai…
Read More
Shugaban MOPPAN na Abuja, Auwal Falala, ya samu ƙaruwar ɗa namiji

Shugaban MOPPAN na Abuja, Auwal Falala, ya samu ƙaruwar ɗa namiji

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Allah Ubangiji ya albarkaci Shugaban Babbar Haɗaɗɗiyar ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Kannywood (MOPPAN) reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, Hon. Auwal Sharif Falala, da samun ƙaruwar ɗa namiji a ranar Lagadi, 6 ga Afrilu, 2025, inda aka raɗa masa suna Muhammad Ashraf Falala ranar da aka yi taron suna bayan mako guda, wato Lahadi, 13 ga Afrilu, 2025. Auwal Falala ya nuna farin cikinsa da samun wannan ƙaruwa, musamman ma kasancewar, jaririn da mahaifiyarsa suna cikin ƙoshin lafiya. Baba Falala yana fitowa a finafinan Hausa masu ƙayatawar, wanda ya kasance ɗaya daga cikin jaruman…
Read More
An yi taron Tarihi da Waƙoƙin Kassu Zurmi a Sakkwato 

An yi taron Tarihi da Waƙoƙin Kassu Zurmi a Sakkwato 

Daga DAHIRU SAMA'ILA a Sokoto Sashen Harsunan Nijeriya na Jami'ar Jihar Sakkwato da ke Birnin Sakkwato ya shirya Taron ƙasa da ƙasa akan tarihin rayuwa da waƙoƙin makaɗa Abubakar Kassu Zurmi.  Taron na kwana huɗu ya gudana ne tsakanin Ranakun Jumu'a 18 zuwa Litinin 21 ga watan Afrilun 2025 a harabar jami'ar da ke Madorawa a birnin Sakkwato. An buɗe bikin mai taken 'Wawa Mugunyar Tsirfa' Tarihin Rayuwa da Waƙoƙin Makaɗa Abubakar Kassu Zurmi a Ranar Asabar 19 /04 2025 tare da samun halartar masana da manazarta daga ciki da kuma wajen Nijeriya. ɗan majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar…
Read More
Bikin auren ‘yar jaruma Zulai Babeji: ‘Yan fim sun mata kara

Bikin auren ‘yar jaruma Zulai Babeji: ‘Yan fim sun mata kara

Daga MUKHTAR YAKUBU Fitacciyar jaruma a masana'antar finafinai ta Kannywood Hajiya Zulai Babeji ta yi bikin auren 'yar autarta, wato Maryam M. Usman Nunu wadda aka fi sani da Maryam 'Yar autar Mama.  Bikin auren dai an fara gudanar da shi ne a ranar Asabar 5 ga Afrilun 2025 inda aka fara da taron liyafa a ɗakin taro na Gidauniyar Jihar Kano da ke kan titin BUK Kano da misalin ƙarfe biyar na yamma. Taron bikin dai ya samu harkar 'yan fim da dama da suka halarci wajen domin taya jaruma Zulai Babeji murna. A wajen taron an sha shagali…
Read More
Kallon finafinai ne ya zaburar da ni na shiga harkar fim – Sayyadi

Kallon finafinai ne ya zaburar da ni na shiga harkar fim – Sayyadi

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Faruk Sayyadi na ɗaya daga cikin zaƙakurai a masanantar Kannywood; ƙwararre ne a fannin zane-zane da tasirin gani (ɓFɗ). Shi darakta ne, kuma marubucin fim ne kuma jarumi ne a masana'antar Kannywood. A wannan hira ta musamman da wakilinmu Ibrahim Hamisu ya yi da shi a Kano, za ku ji tarihinsa da ma wasu muhimman bayanai.  MANHAJA: Za mu so ka gabatar mana da kanka? SAYYADI: Da fari dai, sunana Faruk Sayyadi. An haife ni a unguwar Dandago, kusa da ƴar Maishinkafi. Na yi makarantar firamare a Mawgan, sannan na tafi makarantar sakandare ta Kawaji,…
Read More
Tabbas makomar Kannywood mai kyau ce – Momoh 

Tabbas makomar Kannywood mai kyau ce – Momoh 

"Bayar da gudunmawa ga haɓakar adabin Hausa abu ne da na yi alfahari da shi" Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Aminu Aliyu Shariff Momoh, wanda da aka fi sani da Aminu Momoh na ɗaya daga cikin manyan jarumai kuma fitattu da suka bayar da gagarumar gudunmawa a masana'antar fim ta Kannywood, domin Momoh ya kasance a Kannywood tun shekaru 24 da suka gabata. Don haka za mu iya cewa, ya kasance daga cikin ɗaiɗaikun jaruman da ba sa tsufa a masana'antar Kannywood.  A wannan makon, shafin Nishaɗi na jaridar Blueprint Manhaja ya tattauna da jarumin don samar wa masu karatu…
Read More
Labarin fim ɗin ‘Faliha & Falisha’ ya faru da gaske – Mansurah Isah

Labarin fim ɗin ‘Faliha & Falisha’ ya faru da gaske – Mansurah Isah

DAGA MUKHTAR YAKUBU a Kano A yanzu haka dai shirye-shirye sun yi nisa na fara haska gawurtaccen fim ɗin nan mai suna 'Faliha & Falisha' wanda tsohuwar jaruma kuma furodusa Mansurah Isah ta ɗauki nauyin shiryawa. Fim ɗin wanda ake sa ran za a fara haska shi a sinima a ranar 2 ga Afrilun nan za a nuna shi ne a manyan sinimomi kamar Platinum da ke Kano, Silverbird Kaduna, Silverbird Jabi, Dex View Kano, DexView Katsina, Mees Palace Jos (TBC) Alinco Cinema Ijaye Lagus, Bridge Park Cinema Kaduna, da sauran sinimomi da ke faɗin tarayyar Nijeriya. Domin ganin yadda…
Read More
Gwamnatin Tarayya za ta kafa gidajen al’adu a faɗin ƙasar

Gwamnatin Tarayya za ta kafa gidajen al’adu a faɗin ƙasar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin kafa wuraren al’adu da tarihi a ƙarƙashin nan na nata na ‘Renewed Hope’, wato Sabuwar Nijeriya, a faɗin Nijeriya, domin kiyaye al’adun gargajiyar Najeriya, bunƙasa harkokin yawon buɗe-ido da uwa uba bunƙasar tattalin arziki. Abiola Abdulkareem, mataimaki na musamman ga ministar fasaha, al’adu, da yawon buɗe ido, Hannatu Musawa, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin, a Ilorin, Nihar Kwara. A cewarsa, shirin ya samu amincewar Majalisar Tattalin Arziki ta ƙasa kuma za a aiwatar da shi tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohi domin mayar da wuraren tarihi…
Read More
Ana ci gaba da jimamin rasuwar Jarumin Kannywood, Abdu Kano

Ana ci gaba da jimamin rasuwar Jarumin Kannywood, Abdu Kano

Daga AISHA ASAS A yammacin ranar Talata ne fitaccen jarumin Kannywood, Malam Abdu Kano ko Abdullahi Shu’aibu, wanda aka fi sani da Baba Karƙuzu, ya kwanta dama, inda za mu iya cewa mutuwar tasa ta taɓa mutane da dama, ciki kuwa har da Gwamnatin jiharsa ta Filato, inda jim kaɗan bayan sallar jana’izarsa da aka gudanar da sanyin safiyar ranar Laraba a gidansa da ke Haruna Hadeja Street a Jos, Babban Birnin Jihar Filato, gwamnatin jihar ta fitar da sanarwar jajentawa tare da miƙa ta’aziyyar rasuwar fitaccen Jarumi Baba Karƙuzu ga iyalansa da kuma abokan sana'arsa. A cikin ta’aziyyar mai…
Read More
Darakta Daniel Aboki ya yi amai ya lashe kan Kannywood

Darakta Daniel Aboki ya yi amai ya lashe kan Kannywood

Daga AISHA ASAS  A 'yan kwanakin nan ne aka samu musayar yawu tsakanin ma'abota kallon finafai inda taƙadama kan furucin daraktan shahararren fim ɗin Hausa da ya samu karuwa a duniya, mai suna 'Mai Martaba' wanda ya lashe lambar yabo ta Academy Awards, ta arke kan furucin daraktan na cewa, masana'antar Kannywood da Nollywood sun ƙi shi saboda addininsa da yankinsa.  Wasu waɗanda suka kasance masoya ga daraktan sun musunta maganar inda suke ƙoƙarin kare gwanin nasu, yayin da waɗansu ke ƙoƙarin tabbatar da zancen.  Daraktan fim ɗin 'Mai Martaba', Prince Daniel, fito ya musanta kalaman da ake yaɗawa a…
Read More