Nishadi

Deepika Padukone zata gabatar da fim ɗinta a Gasar Cannes

Deepika Padukone zata gabatar da fim ɗinta a Gasar Cannes

Daga AISHA ASAS  Jaruma Deepika Padukone ta samu tabbaci daga Cannes Film Festival cewa, za ta gabatar da fim ɗinta 'Haske da Duhu' a gasar 2025. Fim ɗin, wanda ke nuna rikicin tunani da ƙyamar mata masu takara a siyasarsu, ya samu goyon baya daga ƙungiyoyin kare haƙƙin mata a Asiya. Deepika ta bayyana cewa: “Na jima ina burin yin wani abu da zai tava zuciyar mata a duniya. Wannan fim yana cike da jin ƙai da adalci.” An shirya fim ɗin tare da Vishal Bhardwaj, kuma za a nuna shi a karon farko a watan Oktoba.
Read More
‘Ya’yan mawaƙi Aminu Ala huɗu sun yi saukar Al’ƙur’ani mai girma

‘Ya’yan mawaƙi Aminu Ala huɗu sun yi saukar Al’ƙur’ani mai girma

Daga MUKHTAR YAKUBU  A ranar Asabar 17/05/2025 ne aka yi taron bikin murnar mahaddatan ƙur'ani da masu sauka da haddar izu goma daidai sama da sha biyar, Makarantar Islamiyya ta Umar Ibn Kattab Unguwar Medile da ke ƙaramar Hukumar kumbotso a Jihar Kano. Taron ya ƙayatar matuƙa gaya domin ya sami halartar manyan mutane na daga malamai da farfesoshi da sakataren ilimi na gwamnati tare da Sarkin ɗiyan Gobir ɗamburan Sarkin Gobir. Aminu Ladan Abubakar Ala. 'Ya'yan Mawaƙi Aminu Ladan Abubakar Ala guda huɗu wato Imammu Zahbi Aminu Ladan Abubakar Ala, Aisha Humaira Aminu Ladan da Amina Aminu Ladan Abubakar…
Read More
Mahaifina ne ya fara bani kuɗin da na yi jarin fim – Amir Iliyasu maiross

Mahaifina ne ya fara bani kuɗin da na yi jarin fim – Amir Iliyasu maiross

DAGA MUKHTAR YAKUBU Amir Iliyasu yana ɗaya daga cikin fitattun jarumai da suke haskawa a cikin shirin 'Dadin Kowa', na tashar Arewa 25 wanda yake fitowa a matsy ɗan daba wato Garzali. Duk da cewa tsohon ɗan fim ne da ya kasance mai shirya finafinai a masana'antar finafinai ta Kannywood wanda ya shirya finafinai da dama irin su 'Jarin Ibo' da 'Asusun Ibro' waɗanda suka shahara a wancan lokacin musamman waƙar 'baba sai mini mai ross a sa a dakin aure na' ta cikin fim ɗin 'Jarin Ibo'. Domin jin ko wanene Amir Iliyasu maiross. Wakilinmu a Kano Mukhtar Yakubu,…
Read More
Dakatar da finafinai 22: CITAD ta gargaɗi hukumar tace finafinan Kano

Dakatar da finafinai 22: CITAD ta gargaɗi hukumar tace finafinan Kano

Daga AISHA ASAS Cibiyar Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma (CITAD) ta bayyana damuwa kan matakin Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano na dakatar da finafinan Kannywood guda 22 da ba da shawara ga gwamnati da ta bi matakin hankali wajen irin waɗannan matakai. A cikin wata sanarwa da Daraktan Gudanarwa na CITAD, YZ Ya’u ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa: “Ko da yake mun gane buƙatar kare tarbiyya da al’adunmu a ɗikin finafinan, dole ne a tabbatar cewa irin wannan mataki ba ya tauye ’yancin sadarwa na ’yan ƙasa ko kuma murkushe ’yancin ƙirƙira da fasaha.” Ya ƙara…
Read More
Sabon rikici a duniyar leƙen asiri: ‘WAR 2’ ya girgiza masana’antar fim

Sabon rikici a duniyar leƙen asiri: ‘WAR 2’ ya girgiza masana’antar fim

Daga AISHA ASAS  Fitaccen kamfanin Yash Raj Films ya saki tallan fim ɗinsa mai dogon zango 'War 2' ranar 20 ga Mayu, 2025, daidai da zagayowar ranar haihuwar tauraron Kudu, Jr NTR. Fim ɗin, wanda Ayan Mukerji ya jagoranta, ya haɗu da ɗimbin yabo da kuma ɗan-karan suka. Hrithik Roshan ya dawo da rawar sa a matsayin Manjo Kabir Dhaliwal, jagoran jami’an leƙen asiri. Amma wannan karon, yana fuskantar sabon maƙiyi: Jr NTR, wanda ke bayyana a karon farko a Bollywood, cikin wani hali na girmamawa da jarumta. “Na ji daɗi sosai da samun damar fuskantar Hrithik a fim ɗaya,”…
Read More
Nollywood na alhinin mutuwar manyan ma’aikatanta biyu

Nollywood na alhinin mutuwar manyan ma’aikatanta biyu

Daga AISHA ASAS  Masana'antar finafinai ta Kudu, wato Nollywood, ta fada cikin yanayin alhini da jimami bayan da aka tabbatar da rasuwar fitattun ma'aikatan kamara guda biyu, Johnson Onoriode Ododife da Chigo Gozman, sakamakon mummunan hatsarin mota da ya faru, yayin da suke dawowa daga bikin aure a birnin Port Harcourt. Rahotanni sun nuna cewa hatsarin ya auku ne da daddare, inda motarsu ta kauce wa hanya ta bugu da bishiya. Kafin isowar jami’an agaji, an tabbatar da mutuwar dukkansu. Hukuma na ci gaba da bincike kan musabbabin hatsarin, yayin da ake ta ƙorafe-ƙorafe game da lalacewar titunan Najeriya. Sanannun…
Read More
Kannywood: Daga gida zuwa duniya – Mafarkin da bai cika ba

Kannywood: Daga gida zuwa duniya – Mafarkin da bai cika ba

Me ke hana Kannywood tsallaka iyakokin Arewa? Daga AISHA ASAS  A cikin shekaru fiye da ashirin da suka gabata, masana’antar finafinan Hausa wadda aka fi sani da Kannywood ta zama wata hanya ta nishaɗi, ilimantarwa da kuma ɗaukaka al’adun Arewa. Finafinai da dama sun ƙayatar da zukatan miliyoyin mutane daga Kano zuwa Katsina, daga Zaria zuwa Zinder. Amma duk da wannan shahara, tambayar da ke ci gaba da yawo tsakanin masana da masu kallo ita ce: "Me ya sa Kannywood ba ta yi amo a duniya ba kamar Nollywood ko Bollywood?" Shin matsalar tana cikin marubuta ne, ko kuma tsari…
Read More
A da ba na sha’awar Kannywood saboda zargin da ake masu – Jaruma Samira Sani

A da ba na sha’awar Kannywood saboda zargin da ake masu – Jaruma Samira Sani

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Samira Sani ƴar asalin garin Kano ce da ta shigo Masanartar Kannywood a shekarar 2022, a tattaunarta da wakilinmu a Kano Ibrahim Hamisu, za ku ji tarihinta da kuma yadda ta daɗe tana mu'amala da ƴan Kannywood kafin ta fara fitowa a fim: MANHAJA:Za mu so ki gabatar da kanki? SAMIRA: Sunana Samira Sani, jaruma a masanartar fim ta Kannywood. Mene ne tarihinki a taƙaice? To ni ƴar asalin garin Kano ce, an haife ni a garin Dakatsalle da ke ƙaramar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano, na yi primary da secondary duk a Dakatsalle, bayan…
Read More
Disney zai fitar da ‘Descendants’ na biyar

Disney zai fitar da ‘Descendants’ na biyar

Daga AISHA ASAS  Kamfanin fina-finai na Disney ya tabbatar da cewa, fim na biyar cikin shahararren jerin Descendants zai fito da suna 'Wicked Wonderland' a shekarar 2026. Wannan sabon fim zai bayyana a tashar Disney Channel da kuma dandamalin Disney+, inda za a ci gaba da labarin ‘ya’yan manyan azzaluman da suka fito daga tatsuniyoyin Disney.  A cikin wannan gawurtaccen fim mai fitowa za a ga fitattun jarumai da suka yi fice a fim ɗin da suka gabata, ciki har da: Brandy Norwood a matsayin Cinderella, Paolo Montalban a matsayin Sarki Charming, Rita Ora a matsayin Sarauniyar Zuciya (ƙueen of…
Read More
EFCC ta gayyaci jaruma Iyabo Ojo da AY Makun kan wulaƙanta Naira 

EFCC ta gayyaci jaruma Iyabo Ojo da AY Makun kan wulaƙanta Naira 

Daga AISHA ASAS  Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) ta gayyaci fitacciyar jarumar fina-finan Nollywood, Iyabo Ojo, da kuma shahararren jarumin barkwanci Ayo Makun (AY) domin yi musu tambayoyi kan yadda aka watsa takardun Naira a fili yayin wasu bukukuwa da suka halarta — abin da ya saɓa wa dokar Najeriya. Iyabo Ojo ta bayyana cewa, EFCC ta gayyace ta bayan bikin ɗiyarta, Priscilla, inda baƙi suka watsa Naira da kuɗaɗen ƙasashen waje. Ta ce tana ƙasar Ingila lokacin gayyatar ta zo, kuma da ta dawo a ranar 5 ga Mayu, 2025, ta halarci ofishin hukumar…
Read More