Rahoto

Rikicin ADC: An yi wa shugaban INEC barazana da takardarsa ta murabus – Farfesa Odinkalu

Rikicin ADC: An yi wa shugaban INEC barazana da takardarsa ta murabus – Farfesa Odinkalu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Fitaccen masanin shari’a, Farfesa Chidi Anselm Odinkalu, ya soki Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC) bisa matakin da ta ɗauka na fassara hukuncin Kotun ɗaukaka ƙara a shari’ar da ke tsakanin jiga-jigan jam'iyyar ADC, Sanata David Mark da Nafiu Bala Gombe da sauransu. A cikin wani saƙo da ya wallafa a dandalin ɗ, Odinkalu ya zargi shugabannin INEC, da shugaba Bola Ahmed Tinubu, da kuma Kotun ɗaukaka ƙara da Babbar Kotun Tarayya da hannu a wani taro da ya ce ya haifar da sanarwar da INEC ta fitar, wadda ke ɗauke da fassarar hukuncin…
Read More
Akpabio ya ayyana kujerun sanatoci uku a matsayin babu kowa

Akpabio ya ayyana kujerun sanatoci uku a matsayin babu kowa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, a ranar Talata ya ayyana kujerun Sanata uku a matsayin babu kowa biyo bayan rasuwar mambobin Majalisar Dattawa ta 10. Mazaɓun da abin ya shafa sun haɗa da Enugu ta Arewa, Nasarawa ta Arewa, da Ribas ta Kudu maso Gabas. Mista Akpabio ya bayyana hakan ne yayin zaman majalisa, inda ya ce guraben sun samu ne sakamakon rasuwar sanatocin da ke wakiltar waɗannan yankuna, bisa tanadin kundin tsarin mulki. “Saboda waɗannan abubuwan bakin ciki da suka faru ga Majalisar Dattawa ta 10, an samar da gurabe domin gudanar da…
Read More
Daular Borno da asalin Kanuri

Daular Borno da asalin Kanuri

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Da farko dai, Jaridar Manhaja ta yi iya bakin ƙoƙari wajen ganin ta kawo wa mai karatu abin da ya inganta daga abin da za mu rubuta ta hanyar tattaro bayanai daga wurare daban-daban da kuma zurfafa bincike; wato cil-da-cil, ganin Annabin tsohuwa. Muna fatan wannan rubutu ya zama fitilar da za ta haskaka zuciyar masu neman sanin haƙiƙanin tarihin ƙabilar Kanurai. A sha karatu lafiya. Daular Borno dai tsohuwar Daula ce a Afirika da aka kafa tun kafin ƙarni na 10 wacce ta haɗa da yankunan da yanzu ke cikin Nijeriya, Nijar, Chadi, Kamaru da…
Read More
Tasirin abokai da ƙawaye

Tasirin abokai da ƙawaye

Tare da BILKISU YUSUF ALI Idan aka ambaci kalmar "aboki" ga namiji,  abin da yake fara zuwa a tunanin mutane shine, wani tsayayyen masoyi wanda kanwarku ke jiƙo wuri guda da shi. Wanda kuma bayan so da yake maka, yana sahun gaba na masu burin ci gabanka da kuma son ganin ka zauna lafiy      a, a gida da waje. Kamar haka kuma yake idan ka ambaci "ƙawa" ga mace. Ko wace rawa abokai da ƙawaye suke takawa a cikin zaman aurenmu? A cikin kowane motsi da dukkan harkokin da mutum zai yi, bayan ya zama baligi, za ka…
Read More
Mene ne sakamakon gwaje-gwajen da masana suka yi kan waken soya?

Mene ne sakamakon gwaje-gwajen da masana suka yi kan waken soya?

(Ci gana daga makon jiya) Daga AISHA ASAS  Sallama dai masu karatu. Muna godiya da bibiyarmu da ku ke yi. Allah Ya amsa addu'o'in mu. Ya sa mun dace da daren Lailatul ƙadar. Barkanmu da Sallah. Allah Ya maimaita. Binciken mako 24: A wani bincike na makonni 24, mata 23 sun sha furotin soya mai ɗauke da isoflavones, yayin da wasu suka sha wani furotin daban. Sakamakon ya nuna: Raguwar tsananin layukan fuska da kashi 7 cikin 100. Rage duhun fata da kashi 2 cikin 100. ƙaruwa a danshin fata har kashi 68 cikin 100 a wani ɓangare na fuska.…
Read More
Soyayya kafin aure: Gari ya waye, amma hankali na barci

Soyayya kafin aure: Gari ya waye, amma hankali na barci

Daga AISHA ASAS  'Soyayya kafin aure, tamkar cin abinci ne a kasuwa, ba a san lafiya ko cutar sa ba' Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Iyali na jaridar Blueprint Manhaja. A wannan makon shafin zai yi dubiya ne kan yadda soyayyar yara kafin aure ke wanzuwa, me ke janyo ta, wane irin lahani take haifarwa, da kuma yadda za a magance ta cikin hikima. Kafin komai zan faro da kai hanakalin mai karatu ga hanyar da rubutun nawa ya karkata. Soyayyar da take rubuce a wasu littafai musamman na Turawa a matsayin wayewa, soyayyar da ke ƙawata…
Read More
Rikicin Gabas ta Tsakiya: Fafaroma Leo ya buƙaci a haramta hare-haren sama

Rikicin Gabas ta Tsakiya: Fafaroma Leo ya buƙaci a haramta hare-haren sama

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Fafaroma Leo, shugaban Cocin Katolika na duniya, ya yi kakkausar suka kan hare-haren boma-bomai daga sama, yana mai cewa, irin waɗannan hare-hare ba su bambance tsakanin fararen hula da mayaƙa, don haka ya kamata a haramta su gabaɗaya. Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin, yayin da yaƙin da ke tsakanin Amurka da Isra’ila da Iran ke shiga mako na huɗu a wani sabon jawabi da ya sake jaddada adawarsa kan yaƙi da tashin hankali. Duk da cewa, bai ambaci wannan rikici kai tsaye ba a wani taro da ya yi da shugabanni da ma’aikatan kamfanin…
Read More
Yadda ’yan siyasa ke jefa matasa bangar soshiyal midiya!

Yadda ’yan siyasa ke jefa matasa bangar soshiyal midiya!

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ana ci gaba da samun sauye-sauye a harkokin siyasa a ƙasar nan, yayin da ake ƙara kusantar Babban Zaɓe na shekarar 2027. 'Yan siyasa, musamman sabbin yanka masu neman a san da su da gwamnoni masu neman tazarce suna ta ƙoƙarin sauyin sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa waccan. Mun ga yadda jihohi irin su Kano, Filato, Adamawa, Taraba da Zamfara gwamnoninsu suka yi sauyin jam'iyya zuwa babbar jam’iyya mai mulki ta APC. Matakin da wasu ke kallo a matsayin wayon a ci ne, wato kowa ƙoƙari yake yi a dama da shi a siyasar tarayya, a…
Read More
Ya hallaka mahaifiyarsa saboda ya ƙi yi masa wanka

Ya hallaka mahaifiyarsa saboda ya ƙi yi masa wanka

Al’ummar ƙauyen Ohatekwe Ukawu da ke ƙaramar Hukumar Onicha a Jihar Ebonyi sun kori wani matashi mai shekaru 20, mai suna Damian Oforbuike, bayan da ake zarginsa da kashe mahaifiyarsa. Rahotanni sun bayyana cewa matashin ya kai wa mahaifiyarsa, Onyemaechi, hari da adda, lamarin da ya jefa al’umma cikin jimami da alhini. An ce wannan mummunan lamari ya faru ne a ƙarshen mako, inda bayan aikata laifin ya tsere zuwa cikin wani daji da ke kusa da ƙauyen. Sai dai matasan yankin sun haɗa kai, inda suka bi sahunsa har cikin dajin, suka kama shi a wurin da yake ɓoye.…
Read More
Jami’ar Dan Fodiyo za ta karɓi baƙuncin taron Tarihi da Waƙoƙin Muhammadu Bawa Dan’anace

Jami’ar Dan Fodiyo za ta karɓi baƙuncin taron Tarihi da Waƙoƙin Muhammadu Bawa Dan’anace

Daga MUHAMMAD HABIB ALHASSAN Cibiyar Nazarin Harshen Hausa ta Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo ta Sokoto ta yi shirin gagarumin taron ƙasa kan tarihi da waƙoƙin Muhammadu Bawa ɗan’anace 'Yartsakkuwa, a Waiwayen Shekaru Arba’in masu Tarin Abubuwan Tunawa a Kansu.  Yanzu haka waɗari ke gudana babu kama hannun yaro a shirye-shiryen amsa kiran Cibiyar Nazarin Harshen Hausa ta Jami’ar Usmanu Dan Fodiyo ta Sokoto zuwa wajen gagarumin taron ƙasa a kan Tarihi da Waƙoƙin Muhammadu Bawa ɗan’anace ‘Yartsakkuwa a Waiwayen Shekaru Arba’in Masu Tarin Abubuwan Tunawa a Kansu.  Wata sanarwa daga Malam Adamu Yunusa Ibrahim, Sakataren kwamitin Shirya taron ta nuna…
Read More