Rahoto

Bankunan Nijeriya 34 sun cika sabbin sharuɗɗan ƙarfafa jari kafin wa’adin CBN

Bankunan Nijeriya 34 sun cika sabbin sharuɗɗan ƙarfafa jari kafin wa’adin CBN

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kwanaki kaɗan kafin cikar wa’adin ranar 31 ga Maris, 2026, ɓangaren bankunan Nijeriya ya samu gagarumin ci gaba bayan da bankuna 34 suka samu nasarar cika sabbin sharuɗɗan ƙarfafa jari da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya gindaya. Binciken da aka gudanar ya nuna cewa mafi yawan bankunan ƙasar, musamman manyan bankuna masu lasisin ƙasa da ƙasa da kuma wasu na ƙasa baki ɗaya, sun tsallake ƙalubalen ƙara jari, abin da ke nuna ɗaya daga cikin manyan nasarori a tarihin harkar kuɗi a Nijeriya. Ana sa ran Babban Bankin zai fitar da cikakken rahoto nan ba da…
Read More
Peter Obi ya sha alwashin farfaɗo da masana’antu da ‘Bankin raya Arewa’ a Kano

Peter Obi ya sha alwashin farfaɗo da masana’antu da ‘Bankin raya Arewa’ a Kano

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Peter Obi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a shekarar 2023, ya yi alƙawarin farfaɗo da masana’antun da ke Kano da dawo da bankin Arewa da aka fi sani da ‘Bank of the North’. Obi ya yi waɗannan kalamai ne a ranar Lahadi a lokacin da ya kai ziyara gidan tsohon gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso, a wani bikin sallah da Kwankwaso ya shirya wanda ya samu halartar ɗaruruwan mutane. Obi ya halarci taron ne tare da gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo da tsohon gwamnan Bayelsa, Seriake Dickson. A yayin da yake…
Read More
Mene ne sakamakon gwaje-gwajen da masana suka yi kan waken soya?

Mene ne sakamakon gwaje-gwajen da masana suka yi kan waken soya?

Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da samun damar ganin zagayowar sati lafiya. Sannunku da jimirin bibiyarmu. Allah Ya barɓi ibadunmu na wannan wata mai alfarma, Ya sa mudace, Ya sa mun dace. Harwayau dai muna nan kan darasinmu na waken soya, wanda yau ya kasance sati na uku akan darasin. Kun dai ji a baya mun bayyana sinadarai da ke tattare a cikin wannan abunci da Allah ya azurta mu da shi, da kuma irin tasirinsa a lafiyar fatarmu tare kuma da yadda ayyukan waɗannan sinadarai ke kama da aikin sinadarin halitta da ke aikin ba wa fata kariya…
Read More
Kwanon maigida daban da na ‘yan gida

Kwanon maigida daban da na ‘yan gida

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS Masu karatu idan ku na biye da mu, kun ji yadda baƙuwarmu ta koro bayani kan wannan darasi na mu, ta bayyana asali da kuma yadda wannan ɗabi'a ke tasiri ga tarbiyya da kuma dukiyarmu. A wannan satin za mu ba ta dama don ta kawo mana mafita kan wannan matsala, domin dai an ce babu damuwar da ba ta da magani, ko a hannun mutum ko ta wurin wanda ya yi mutum. SA'ADATU SAMINU KANKIA ce a shafin na iyali: Ta yaya kike ganin za a iya shawo kan wannan matsala?…
Read More
Abin da ya kamata mace mai aiki ta sani

Abin da ya kamata mace mai aiki ta sani

Tare da BILKISU YUSUF ALI Aure yarjejeniya ce ta zaman tare na iyali wanda ake sa ran kwanciyar hankali da nutsuwa cikinta. Babbar ribar da ake fata da an yi aure ita ce samun iyali; iyali kuwa nagartattu su ne abin nema, don gina rayuwar al’umma masu tasowa. Mata sune ginshiƙi na kula da gida da ma maigidan da ‘ya’yan gida da ma duk wani wanda ke mu’amala da gidam. Mace da ke fita aiki sawa’un aikin nan na gwamnati ne ko kuma akasin haka tana da ƙalubale inda wasu ke hangen wannan fita da ta ke yi abu ne…
Read More
Ko kun san dakarun mata zalla da suka yaƙi Turawan mulkin mallaka?

Ko kun san dakarun mata zalla da suka yaƙi Turawan mulkin mallaka?

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD A yau ma dai jaridar Manhaja ta sake binciko wani ƙayataccen tarihin da ba kowa ya san da zamansa ba, wannan tarihi na wasu jaruman dakarun mata mayaƙa ne da aka yi a Dahomey, waɗanda aka fi sani da ‘Amazons’ a bayyana. Ficen da masarautar Dahomey ya yi tsakanin ƙarni na 17-19, da a yau ake kira Jamhuriyar Benin, ya samu ne saboda kafa wata rundunar mayaƙa da ta ƙunshi mata zalla, waɗanda ake kira ‘Dahomey Amazon’. Yankin Dahomey wanda ke a ƙasar da ake kira Benin a yau, yanki ne mai ɗumbin tarihi daga cikin…
Read More
Shin waka da fim haram ne ko halal?

Shin waka da fim haram ne ko halal?

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Sakamakon tambaya da wani ya yi, cewar to wai ta ina ma ita harkar Fim ta sami wani halasci daga Qurani, Hadisi, ko ijtihadin Malamai? Sai na ga ya kamata na bada amsar tambayar tasa domin mahimmancinta, kuma domin a gane cewa shin a mahangar musulunci, shi kansa film din halal ne ko Haram? Abu na farko da zamu fara fahimta shine Allah ya ce mana; Q6:38 "...Ba mu yi sakacin barin komai ba cikin littafi (Quran)." Wato Qurani ya zo da duk wani hukunci, halal ko Haram, a kan duk wani abu da Allah ya…
Read More
Mutane da dama sun mutu bayan fashewar bom a Kwara

Mutane da dama sun mutu bayan fashewar bom a Kwara

Daga USMAN KAROFI Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon fashewar bam da ya rutsa da wata motar haya kusa da ƙauyen Woro, a ƙaramar hukumar Kaiama, Jihar Kwara. Wannan lamari ya faru da safiyar Litinin, 23 ga Maris 2026, da misalin ƙarfe 7:43 na safe, lokacin da motar ke tafe daga ƙauyen Wurumakoto zuwa New Bussa a Jihar Neja. Direban motar, Malam Zubairu, ya yi tafiya ba tare da sani ba a kan bama-bamai da aka saka, wanda suka fashe nan take a kan motar. Fashewar ta kashe direban nan take, sannan ta jikkata wasu fasinjoji sosai,…
Read More
ADC ta yi barazanar kai ƙara ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam kan tsare El-Rufai

ADC ta yi barazanar kai ƙara ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam kan tsare El-Rufai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai, a matsayin take haƙƙin ɗan adam mai tsanani. Jam’iyyar ta ce ana tsare da El-Rufai a hannun Hukumar ICPC tsawon kwanaki sama da 30, lamarin da ta bayyana a matsayin wanda ya saba doka da kundin tsarin mulki. A cikin wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba, ADC ta zargi hukumomin tsaro da ƙoƙarin tilasta wa El-Rufai sauya matsayinsa na siyasa ta hanyar matsin lamba. Jam’iyyar ta bukaci ICPC da ta mutunta dokar ƙasa…
Read More