Rahoto

Muhimmancin haɗin kai a cikin al’umma

Muhimmancin haɗin kai a cikin al’umma

Tare da BILKISU YUSUF ALI Haɗin kai yana daga cikin manyan ginshiƙai da suke tabbatar da zaman lafiya, cigaba da ɗorewar kowace irin al’umma. Al’umma ba ta iya bunƙasa sai idan mutane suna yin aiki a tare, suna girmama juna, suna taimakon juna tare da fifita muradun kowa a kan na kansa. A tarihi da al’adance, Hausawa sun gina rayuwarsu bisa haɗin kai, wanda ya bayyana ta hanyar karin maganganu kamar “Hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka” da “Taimakon juna ke kawo arziƙi”. Ma’anar haɗin kai Haɗin kai na nufin aiki tare tsakanin mutane ko ƙungiyoyi domin cimma wata manufa…
Read More
Tarihi da gwagwarmayar Nelson Mandela

Tarihi da gwagwarmayar Nelson Mandela

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD An haifi Nelson Rohlihlahla Mandela ne a ranar 18 ga watan Yulin 1918 a ƙauyen Mɓezo na yankin Umtata wanda a lokacin ya ke lardin Cape na ƙasar Afirka ta kudu. Asalin sunan da mahaifinsa ya naɗa masa shi ne ‘Rolihlahla’ wanda a yaren ƙabilarsa ta ɗhosa yana nufin ‘mai ƙiriniya’ ko ‘neman fitina’ wanda kuma daga baya lalle sunan ya bi shi saboda irin ƙiriniyar da aka ce yana da shi tun yana ƙarami sannan kuma ya ci gaba da binsa wanda ana ganin yana daga cikin abubuwan da suka sanya shi shiga ƙungiyoyin fafutuka…
Read More
Yadda dillalan gidaje ke cutar da masu neman haya a Abuja – Bincike

Yadda dillalan gidaje ke cutar da masu neman haya a Abuja – Bincike

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Matsalar tsadar gidaje da ke addabar mazauna Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja, da kuma wasu manyan biranen Nijeriya na ci gaba da tsananta, inda wani bincike ya nuna cewa wasu dillalan gidaje marasa ƙwarewa suna amfani da damar da ke tattare da ƙarancin gidaje domin cutar da masu neman haya. Binciken ya nuna cewa ayyukan da ba su dace ba da wasu dillalan gidaje ke yi suna taka rawa wajen ƙara tsadar haya, tare da jefa masu neman gidaje cikin halin ƙunci. A birane kamar Legas, Fatakwal da Kano, masu neman gidaje kan gamu da ƙalubale…
Read More
Ashraf Mahrous: Jarumin ɗan Masar da ya ja jirgi mai nauyin tan 700 da haƙoransa

Ashraf Mahrous: Jarumin ɗan Masar da ya ja jirgi mai nauyin tan 700 da haƙoransa

Wani ɗan dambe daga ƙasar Masar mai suna Ashraf Mahrous ya jawo hankalin duniya bayan da ya ja jirgi mai nauyin tan 700 (kusan kilo 635,000) da haƙoransa a gaɓar tekun Hurghada da ke yankin Bahar Maliya. Mahrous, wanda ake kira “Kabonga”, kuma aka fi saninsa da laƙabin “Jarumi Mai ƙarfi” a Masar, ya kuma ci gaba da jan wasu jiragen ruwa biyu tare da nauyin tan 1,150 (fiye da kilo miliyan ɗaya) gaba ɗaya. “Na zo yau domin kafa tarihi a duniya,” inji Mahrous bayan gwajin. “Na jawo su duka, da taimakon Allah, domin in tabbatar wa duniya cewa…
Read More
Nauyin bashi na ci gaba da matsin lamba ga tattalin arzikin Nijeriya – Rahoto

Nauyin bashi na ci gaba da matsin lamba ga tattalin arzikin Nijeriya – Rahoto

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Matsin tattalin arziƙi na ci gaba da ƙara tsananta wa Nijeriya yayin da kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ke kashewa wajen biyan bashin ƙasa suka zarce kuɗin da ake warewa domin ayyukan raya ƙasa da kimanin Naira tiriliyan 3.9 a cikin shekaru biyu da suka gabata. Rahoton bayani da jaridar News Point Nigeria ta samu daga Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya ya nuna cewa gwamnatin tarayya ta kashe jimillar Naira tiriliyan 27.2 wajen biyan bashi tsakanin shekarun 2024 da 2025. Wannan na nuni da yadda nauyin bashi ke ƙara danna tattalin arzikin ƙasar. Takardar bayanin, wadda Mai Ba…
Read More
Annobar tsutsa na barazana ga noman tumatiri a Kano, inji manoma rani

Annobar tsutsa na barazana ga noman tumatiri a Kano, inji manoma rani

Daga DAUDA USMAN Kungiyar Manoman Rani a jihar Kano ta bayyana damuwarta kan wata annoba ta tsutsa mai suna Sharon wadda ke lalata gonakin tumatiri, lamarin da ke janyo asarar maƙudan kuɗi ga manoma a duk shekara. Shugabannin ƙungiyar sun yi kira ga gwamnatin jihar Kano da ta gaggauta ɗaukar mataki domin nemo maganin da zai kawo ƙarshen wannan matsala. Shugabannin ƙungiyar manoman rani ta ƙasa da kuma na reshen jihar Kano da ke yankin kasuwar ‘Yan Gwari ta Kwanar Gafan a ƙaramar hukumar Garun Malam ne suka bayyana haka yayin wani taron ƙungiyar da aka gudanar a Kano ranar…
Read More
Rashin tsaro barazana ce ga tattalin arzikin Arewa — NYEEF

Rashin tsaro barazana ce ga tattalin arzikin Arewa — NYEEF

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar ƙarfafa Matasan Arewa da Wayar Musu da Kai, wato Northern Youth Empowerment & Enlightenment Forum (NYEEF), ta fitar da wata muhimmiyar sanarwar manufofi bayan kammala Taron Tattaunawa na Shekara karo na uku da ta gudanar a watan Janairun 2026 a jihar Kaduna. Taron, wanda aka shirya domin karrama marigayi Alhaji Suleiman Abubakar Uban Doman Gudu, tsohon Daraktan Harkokin Sarauta na ƙungiyar, ya haɗa manyan malamai, shugabannin addini, kwararrun harkokin tsaro, masu tsara manufofi, shugabannin matasa da kuma ‘yan jarida domin nazarin manyan matsalolin da ke addabar Arewacin Nijeriya da ma kasa baki ɗaya. A sanarwar…
Read More
Yara miliyan 6.4 na fama matsanancin rashin abinci a Arewacin Nijeriya — ICRC

Yara miliyan 6.4 na fama matsanancin rashin abinci a Arewacin Nijeriya — ICRC

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD ƙungiyar Bayar da Agaji ta Duniya, wato International Committee of the Red Cross (ICRC), ta bayyana damuwa kan ƙaruwar matsalar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara a yankunan da ke fama da rikici a Arewacin Nijeriya. ƙungiyar ta ce, kimanin yara miliyan 6.4 ’yan ƙasa da shekara biyar a yankunan Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya ne ke fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki. A cewar ƙungiyar, rikicin da aka shafe kusan shekara 15 ana yi ya lalata rayuwar jama’a, noma da samar da abinci, wanda ya sa…
Read More
Asalin tarihin rikicin Iran da Isra’ila

Asalin tarihin rikicin Iran da Isra’ila

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rikicin da ya dabaibaye Iran da Israel bai samo asali daga yau ba. Ya samo tushe ne tun daga sauyin gwamnati da ya girgiza yankin Gabas ta Tsakiya a shekarar 1979, lokacin da juyin-juya halin Musulunci ya kawo ƙarshen mulkin Shah tare da kafa Jamhuriyar Musulunci a Tehran.  Amma kafin wannan lokaci, dangantakar ƙasashen biyu ta kasance mai kyau, har ma ana kallon Iran a matsayin ɗaya daga cikin ƙawayen ɓoye na Isra’ila a yankin. Kawance a zamanin Shah: A ƙarƙashin mulkin gidan sarautar Pahlavi, musamman a zamanin Shah Mohammad Reza Pahlavi, Iran ta kasance kusa…
Read More
Gudunmawar iyaye wajen nasarar ’ya’yansu a makaranta

Gudunmawar iyaye wajen nasarar ’ya’yansu a makaranta

Tare da BILKISU YUSUF ALI Iyaye suna da rawar gani sosai wajen tabbatar da nasarar ‘ya’yansu a makaranta. Rashin kulawa ko rashin goyon baya daga iyaye kan iya shafar karatun ɗalibai ta hanyoyi da dama, yayin da kulawa da haɗin kai tsakanin iyaye da makaranta ke ƙara wa ɗalibai ƙarfi da ƙwarin gwiwa wajen cimma burinsu.  Muhimman abubuwan da iyaye za su yi don taimakawa nasarar ‘ya’ya 1.Kulawa da yanayin karatu a gida Iyaye su tabbatar cewa suna samar wa ‘ya’yansu wuri mai kyau da kwanciyar hankali domin karatu. Hakan yana taimakawa wajen mayar da hankali da samun sakamako mai…
Read More