Labarai

Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Shugaba guda huɗu da rage harajin kiran waya da kashi biyar cikin 100

Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Shugaba guda huɗu da rage harajin kiran waya da kashi biyar cikin 100

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya sa hannu a kan umarnin shugaba guda huɗu, da nufin rage wasu nau'o'in haraje-haraje ga al'ummar ƙasar. Ɗaya daga cikin umarnin shugaban ƙasar shi ne dakatar da harajin kashi biyar a kan ayyukan wayoyin sadarwa da kuma dakatar da harajin da aka tsawwala a kan kayan da ake sarrafawa a cikin gida. Mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan ayyuka na musamman da al'amuran sadarwa, Dele Alake ya faɗa ranar Alhamis cewa shugaban ƙasar ya kuma sa hannu a kan Dokar Kuɗi ta 2023, wadda a yanzu ta jingine…
Read More
Tinubu bai fitar da jerin sunayen ministoci ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Tinubu bai fitar da jerin sunayen ministoci ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Alhamis Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa, ba a kammala shirya jerin sunayen ministocin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai naɗa ba. Mataimakin Musamman ga Shugaban Ƙasa kan ayyuka na musamman, sadarwa da dabaru, Dele Alake, ne ya bayyana haka a yayin ganawa da manema labarai a fadar gwamnati da ke Abuja. Alake ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da jita-jitar da ke tattare da jerin sunayen ministocin da ake jira. "Game da jerin ministocin, babu gaskiya a cikin duk waɗannan abubuwan," inji Alake. "Lokacin da Shugaban Ƙasa ya natsu…
Read More
Ba zan wahalar da ’yan Nijeriya kamar gwamnatin Buhari ba – Tinubu

Ba zan wahalar da ’yan Nijeriya kamar gwamnatin Buhari ba – Tinubu

*Ya rage harajin da aka ƙaƙaba na shigo da motoci da sauransu  Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sauya wasu harajin da aka sanya a cikin mintunan ƙarshe da tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rattava wa hannu, yana mai cewa ba zai shaƙe ‘yan Nijeriya ya wahalar da su kamar yadda gwamnatin baya ta yi ba. Shugaban ya soke harajin ne a cikin umarnin zartarwa a jiya Alhamis, 6 ga Yuli, 2023. Harajin sun haɗa da dakatar da harajin kashi 5 da ake cece-kuce kan ayyukan sadarwa; Harajin Kore na kashi 10…
Read More
Hamayya da neman karɓe kujerata ta Sanata ɗimuwa ce kawai – Rufa’i Hanga

Hamayya da neman karɓe kujerata ta Sanata ɗimuwa ce kawai – Rufa’i Hanga

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Sanata Rufa'i Sani Hanga ya bayyana cewa masu hamayya akan kujerarsa ta Sanatan Kano ta Tsakiya "in ba su yi hamayya ba, ba su yi halasci ba domin dama abinda ita siyasa ta gada kenan abinda rayuwa ta gada kenan." Ya bayyana haka ne da yake zantawa da 'yan jarida a Kano, inda ya ce ba yadda za ka yi da ɗan hamayya mutum dole ko waye kai dole ka samu maƙiya da masoya, sai dai kullum fata shine masoya su fi maƙiya yawa. Ya ce shi baya jin ciwon hamayya ko abinda ake faɗa…
Read More
Masarautar Zazzau ta dakatar da Hakimi kan zargin lakaɗa wa matashi duka

Masarautar Zazzau ta dakatar da Hakimi kan zargin lakaɗa wa matashi duka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Masarautar Zazzau ta dakatar da Alhaji Mustapha Adamu Ubaidullah daga kujerarsa ta Marafan Yamman Zazzau. Masarautar ta ce ɗaukar matakin ya biyo bayan koken da al’ummar Unguwar Magajiya da ke birnin Zariya suka miƙa, na zargin cin zarafin wani mutum da ake yi wa basaraken. A takardar sanarwar da mai magana da yawunta, Abdullahi Aliyu Ƙwarbai ya fitar ranar Talata, masarautar ta ce ta amince cikin gaggawa ta dakatar da Hakimin har sai abin da hali ya yi a nan gaba. Shi dai Alhaji Mustapha, majalisar ta same shi ne da laifin zartar…
Read More
A karon farko an naɗa mace Alƙalin-alƙalai a tarihin Kano

A karon farko an naɗa mace Alƙalin-alƙalai a tarihin Kano

Daga BASHIR ISAH A ranar Alhamis da ta gabata Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tabbatar da naɗin Dije Aboki a matsayin Alƙalin-Alƙalan Jihar Kano. Wannan naɗi ya zama al'amari na tarihi a jihar, kasancewar Dije ce mace ta farko da za ta riƙe wannan matsayi a jihar ta Kano. Naɗin nata ya biyo bayan wasiƙar da Gwamna Abba Yusuf ya aike wa majalisar jihar wadda aka gabatar da ita a zauren majalisar a ranar Alhamis. Shugaban Majalisar, Ismail Falgore, shi ne ya karanto wasiƙar yayin zaman majalisar a ranar Alhamis da ta gabata. Da fari, an naɗa Dije Muƙaddashin Alƙalin-alƙalan…
Read More
Amarya ta yi ajalin angonta a Bauchi

Amarya ta yi ajalin angonta a Bauchi

Wata amarya mai suna Maimuna Suleiman 'yar shekaru 21, ta kashe mijinta Aliyu Muhammad ta hanyar daɓa masa wuƙa a unguwar Ƙofar Ɗumi dake Bauchi. 'Yan sandan yankin sun tabbatar da aukuwar hakan tare da cewa, suna tsare da amaryar don zurfafa bincike. Mai magana da yawun 'yan sanda na Bauchi, ASP Aminu Gimba Ahmed ya ce lamarin ya faru ne ranar 5 ga Yulin 2023 da misalin ƙarfe 6:00 na yamma. Ya ƙara da cewa, bayan da suka samu labari sun garzaya gidan inda suka ɗauki mijin da matar zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa (ABUTH). Ya…
Read More
Sarkin Rano yana bada kulawa sosai wajen kare kimar al’adun mu – Uban Doman Rano

Sarkin Rano yana bada kulawa sosai wajen kare kimar al’adun mu – Uban Doman Rano

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An bayyana cewa Sarkin Rano, Alhaji Kabiru Autan Bawo da cewa yana kan gaba wajen himmatuwa da bada kulawa wajen ɗabbaƙa raya al'adun mu na gargajiya. Mataimakin Sufeto Janar na 'Yan sanda mai kula da sashen sufuri, Yusuf Usman Chiromawa. Uban Doman Rano. Walin Garun Malam shine ya bayyana hakan da yake zantawa da 'yan jarida. Ya ce koda shiga ta Ado da Autan Bawo Sarkin Rano yake a koyaushe yana wakiltar suturar al'dummu na gargajiya ne, duk wani abu na cigaba yana ƙoƙari ya ga ya tafi da tsari na al'adarmu don kiyaye kimar…
Read More
Zaɓar Asma’u Inuwa a matsayin Shugabar Matan Gwamnonin Arewa sara ne kan gaɓa – Esther Amisu

Zaɓar Asma’u Inuwa a matsayin Shugabar Matan Gwamnonin Arewa sara ne kan gaɓa – Esther Amisu

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Esther Amisu, 'yar siyasa ce a jihar Gombe kuma ƙwararriya a ɓangaren sanin harkokin siyasa, ta ce ba shakka matan Gwamnonin Arewa ba su yi zaɓen tumun dare ba na zaɓar Hajiya Asma'u Muhammad Inuwa Yahaya, uwargidan gwamnan Gombe a matsayin jagora. Esther Amisu, ta ce zaɓar Asma'u Inuwa Yahaya da matan gwamnonin suka yi zai ƙara bai wa mata dama na shiga harkokin siyasa domin Asma'u mace ce da a kullum take ƙoƙarin mata sun samu kulawa ta musamman an kuma basu wani kaso mai tsoka a muqaman siyasa. Ta yi wannan batu…
Read More
Raɗɗa ya saka hannu kan yarjejeniya da UNDP don inganta tsaro a Jihar Katsina

Raɗɗa ya saka hannu kan yarjejeniya da UNDP don inganta tsaro a Jihar Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya saka hannu a kan yarjejeniyar fahimtar juna da Hukumar Raya Ƙasa ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNDP don ƙaddamar da cibiyar bayar da kariya a Arewa maso Yammacin Nijeriya. Taron mai ɗumbin tarihi ya gudana ne a ɗakin taro na Majalisar Ɗinkin Duniya dake Abuja. Cibiyar samar da tsaro yankin Arewa maso yamma shiri ne na hukumar UNDP Nijeriya. Ma’aikatar harkokin waje da ofishin jakadancin Norway ne ke ɗaukar nauyin shirin dake da nufin tallafa wa jihohin Sakkwato, Zamfara, da Katsina. Shirin na neman yin amfani da matakan…
Read More