Babban Labari

Juyin mulkin Gabon ya kaɗa hantar shugabannin Afrika

Juyin mulkin Gabon ya kaɗa hantar shugabannin Afrika

•Ba za mu amince da halayyar sojoji ba, inji Shugaban Nijeriya*Shugabannin Kamaru da Rwanda sun sauke manyan hafsoshinsu*Ka daure ka koma Nijar – Tinubu ya roqi Sarkin Musulmi*Hamɓararren Shugaban Gabon ya nemi agaji Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu hamvarar da gwamnatin Ƙasar Gabon ya ɗaga hankalin wasu shugabannin Afrika bisa la’akari da yadda suke ɗaukar matakai daban-daban wajen ganin sun daƙile afkuwar hakan a ƙasashensu, inda ake ganin lamarin a matsayin kaɗuwar hanta. A shekaranjiya Laraba, 30 ga Agusta, 2023, ne sojoji suka hamɓarar da gwamnatin Ƙasar Gabon, makonni bayan kiki-kakar da ake yi da sojojin…
Read More
Malagi: Kakakin Nupe kuma kakakin Nijeriya

Malagi: Kakakin Nupe kuma kakakin Nijeriya

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A ranar Litinin, 21 ga Agusta, 2023, ne Shugaban kamfanin gidajen jaridun Blueprint da Manhaja kuma Kakakin Masarautar Nupe, Alhaji Mohammed Idris, wanda ake yi wa laƙabi da Malagi, ya kama aiki a matsayin Ministan Labarai na Tarayyar Nijeriya, inda hakan ke nuni da cewa, baya ga kasancewarsa Kakakin Nupe, a yanzu kuma shine Kakakin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya. Wannan ya biyo bayan miƙa sunan Malagi da Shugaban Nijeriya Ahmed Bola Tinubu ya yi ga Majalisar Dattawar Nijeriya, wacce ta tantance Malagin tare da tabbatar da shi a matsayin minista a Nijeriya. Shin wane ne…
Read More
Shugaba Tinubu ya rantsar da ministocinsa

Shugaba Tinubu ya rantsar da ministocinsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Nyesom Wike da wasu 44 a matsayin ministocinsa a hukumance. Bikin rantsarwar ya gudana ne ranar Litinin a babban zauren taron Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. An raba ministocin ne zuwa rukuni bakwai sannan aka rantsar da su rukuni bayan rukuni. Runkunin farko da aka rantsar ya ƙunshi Babban Lauyan Ƙasa kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi, Ƙaramar Ministar Ƙwadago Nkiruka Onyejeocha, Ƙaramin Ministan Gas a Ma'aikatar Albarkatun Fetur, Ekperikpe Ekpo, Ministar Harkokin Mata, Uju Kennedy da kuma Ministan Ilimi, Tahir Maman. Sai rukuni na biyu da ya ƙunshi…
Read More
Ma’aikatun ministoci:Yadda Tinubu ya shammaci ’yan Nijeriya

Ma’aikatun ministoci:Yadda Tinubu ya shammaci ’yan Nijeriya

*Malagi da sauran ministoci za su sha rantsuwa ranar Litinin*A karon farko Kano ba ta da babban minista*Ɗan Kudu ya zama Ministan Abuja bayan shekaru masu yawa*Tsohon gwamna ya zama ƙaramin minista*Wataƙila Gawuna ya samu kujerar babban minista daga Kano Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Laraba, 16 ga Agusta, 2023, Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya shammaci masu lura da al’amuran yau da kullum da sauran al’ummar ƙasar bayan da ya sanar da ma’aikatun da sababbin ministocinsa za su jagoranta. Shugaba Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa a ranar Litinin, 21 ga Agusta, 2023. Ministocin da za…
Read More
Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Tinubu zai rantsar da ministoci makon gobe

Daga BASHIR ISAH Ya zuwa ranar Litinin ta makon gobe idan Allah Ya kai mu ake sa ran Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai rantsar da sabbin ministocinsa da ya naɗa. Sanarwar da ta fito ta bakin Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ta ce bikin rantsarwa zai gudana ne a babban zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da misalin ƙarfe 10 na safe. Sanarwar ta ƙara da cewa 'yan rakiya biyu-biyu kacal aka amince wa ministocin su take musu baya zuwa wajen taron. “Ana sa ran ministocin kowanne ya zo da 'yan rikiya guda biyu. “Sannan…
Read More
Gwamnati ta sake maka Emefiele a kotu kan zargin laifuffuka 20

Gwamnati ta sake maka Emefiele a kotu kan zargin laifuffuka 20

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta sake maka tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele a kotu inda take tuhumarsa da aikata laifuka 20. Wannan na zuwa ne bayan shigar da buƙatar janye ƙarar "mallakar bindiga ta haramtacciyar hanya" da gwamnatin ta shigar da fari kan Emefiele ɗin a Babban Kotun da ke zamanta a Legas. Daraktan sashen shigar da ƙararraki (DPP) a Ma'aikatar Shari'a ta Ƙasa, Mohammed Abubakar, ya sahaida wa alƙalin kotun, Nicholas Oweibo, cewar buƙatar janye ƙarar daga ɓangaren gwamnati ta taso ne domin ba da damar zurfafa bincike.…
Read More
Yaƙi na shirin ɓarkewa tsakanin ECOWAS da Nijar

Yaƙi na shirin ɓarkewa tsakanin ECOWAS da Nijar

*Ƙungiyar ECOWAS ta umarci dakarunta su yi shirin ko-ta-kwana*Tinubu ya aike da malaman Musulunci Nijar don shiga tsakani*Mu na bin Nijar bashin Naira Biliyan huɗu na lantarki, inji Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu matuƙar al’amura ba su sauya ba, yaƙi yana shirin varkewa tsakanin Ƙungiyar Tattalin Arziki ta Ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) ƙarƙashin jagorancin Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, da sojojin da suke riqe da madafun iko a Ƙasar Nijar bayan sun kifar da halastacciyar gwamnatin dimukraɗiyya a ƙarƙashin jagorancin Mohamed Bazoum, wanda sojojin suka hamɓarar. Hakan ya biyo bayan yadda shugabannin Ƙasashen ECOWAS…
Read More
Majalisa ta tabbatar da Malagi a matsayin Minista

Majalisa ta tabbatar da Malagi a matsayin Minista

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta tabbatar da mawallafin Jaridun Blueprint da Manhaja, Mohammed Idris Malagi daga Jihar Neja a matsayin Minista a Gwamnatin Bola Tinubu. Wannan na zuwa ne bayan shafi kimanin mako guda da Majalisar Dattawa ta yi tana tantance sunayen da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya aike mata don naɗa su muƙaman ministoci. Daga cikin waɗanda suka bi sawun Malagi wajen tabbatar da su a matsayin minista har da Dele Alake (Ekiti), tsohon Gwamnan Jihar Ribas Governor Nyesom Wike da tsohon minista a gwamnatin Muhammadu Buhari, Festus Keyamo, SAN, da sauransu. Malagi, Alake da Wike na daga…
Read More
NLC ta dakatar da ƙudirin tafiya yajin aiki – Fadar Shugaban Ƙasa

NLC ta dakatar da ƙudirin tafiya yajin aiki – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga BASHIR ISAH Fadar Shugaban Ƙasa ta ce Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) da ta 'yan Kasuwa (TUC) sun amice da su dakatar da ci gaba zanga-zangar da suka fara. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Mista Dele Alake, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar a Abuja. Ya ce an cim ma hakan ne biyo bayan tattauna da ƙungiyoyin suka yi da Shugaba Tinubu inda suka nuna gamsuwarsu dangane da tabbacin da Shugaban ya ba su na cim ma buƙatunsu. Yayin tattaunawar, Comrade Joe Ajaero ne ya jagoranci ɓangaren NLC, yayin da Comrade Festus Usifo ya…
Read More
Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi a yau

Tinubu zai yi wa ‘yan ƙasa jawabi a yau

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu zai yi wa 'yan ƙasa jawabi da misalin ƙarfi 07:00 na dare yau Litinin. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da ta fito ta bakin mai bai wa Tinubu shawara kan ayyuka na musamman da harkokin sadarwa, Dele Alake. Sanarwar ta ce ana buƙatar gidajen talabijin da rediyo da sauransu, da su jona da Tashar Talabijin ta Ƙasa da kuma Tashar Rediyo ta ƙasa don yaɗa jawabin Shugaba Ƙasar kai tsaye. Sai dai sanarwar ba ta fayyace dalilin da ya sa Tinubun zai yi 'yan ƙasa jawabin ba.
Read More